< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
oratio pauperis cum anxius fuerit et coram Domino effuderit precem suam Domine exaudi orationem meam et clamor meus ad te veniat
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
non avertas faciem tuam a me in quacumque die tribulor inclina ad me aurem tuam in quacumque die invocavero te velociter exaudi me
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
quia defecerunt sicut fumus dies mei et ossa mea sicut gremium aruerunt
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
percussum est ut faenum et aruit cor meum quia oblitus sum comedere panem meum
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
a voce gemitus mei adhesit os meum carni meae
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
similis factus sum pelicano solitudinis factus sum sicut nycticorax in domicilio
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
vigilavi et factus sum sicut passer solitarius in tecto
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
tota die exprobrabant mihi inimici mei et qui laudabant me adversus me iurabant
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
quia cinerem tamquam panem manducavi et poculum meum cum fletu miscebam
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
a facie irae et indignationis tuae quia elevans adlisisti me
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
dies mei sicut umbra declinaverunt et ego sicut faenum arui
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
tu autem Domine in aeternum permanes et memoriale tuum in generationem et generationem
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
tu exsurgens misereberis Sion quia tempus miserendi eius quia venit tempus
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
quoniam placuerunt servis tuis lapides eius et terrae eius miserebuntur
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
et timebunt gentes nomen Domini et omnes reges terrae gloriam tuam
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
quia aedificabit Dominus Sion et videbitur in gloria sua
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
respexit in orationem humilium et non sprevit precem eorum
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
scribantur haec in generationem alteram et populus qui creabitur laudabit Dominum
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
quia prospexit de excelso sancto suo Dominus de caelo in terram aspexit
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
ut audiret gemitum conpeditorum ut solvat filios interemptorum
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
ut adnuntiet in Sion nomen Domini et laudem suam in Hierusalem
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
in conveniendo populos in unum et reges ut serviant Domino
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
respondit ei in via virtutis suae paucitatem dierum meorum nuntia mihi
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
ne revoces me in dimidio dierum meorum in generationem et generationem anni tui
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
initio tu Domine terram fundasti et opera manuum tuarum sunt caeli
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
ipsi peribunt tu autem permanes et omnes sicut vestimentum veterescent et sicut opertorium mutabis eos et mutabuntur
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
tu autem idem ipse es et anni tui non deficient
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
filii servorum tuorum habitabunt et semen eorum in saeculum dirigetur