< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Oratio pauperis, cum anxius fuerit, et in conspectu Domini effuderit precem suam. [Domine, exaudi orationem meam, et clamor meus ad te veniat.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Non avertas faciem tuam a me: in quacumque die tribulor, inclina ad me aurem tuam; in quacumque die invocavero te, velociter exaudi me.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Quia defecerunt sicut fumus dies mei, et ossa mea sicut cremium aruerunt.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Percussus sum ut fœnum, et aruit cor meum, quia oblitus sum comedere panem meum.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
A voce gemitus mei adhæsit os meum carni meæ.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Similis factus sum pellicano solitudinis; factus sum sicut nycticorax in domicilio.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Vigilavi, et factus sum sicut passer solitarius in tecto.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Tota die exprobrabant mihi inimici mei, et qui laudabant me adversum me jurabant:
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
quia cinerem tamquam panem manducabam, et potum meum cum fletu miscebam,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
a facie iræ et indignationis tuæ: quia elevans allisisti me.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Dies mei sicut umbra declinaverunt, et ego sicut fœnum arui.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Tu autem, Domine, in æternum permanes, et memoriale tuum in generationem et generationem.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Tu exsurgens misereberis Sion, quia tempus miserendi ejus, quia venit tempus:
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
quoniam placuerunt servis tuis lapides ejus, et terræ ejus miserebuntur.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Et timebunt gentes nomen tuum, Domine, et omnes reges terræ gloriam tuam:
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
quia ædificavit Dominus Sion, et videbitur in gloria sua.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Respexit in orationem humilium et non sprevit precem eorum.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Scribantur hæc in generatione altera, et populus qui creabitur laudabit Dominum.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Quia prospexit de excelso sancto suo; Dominus de cælo in terram aspexit:
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
ut audiret gemitus compeditorum; ut solveret filios interemptorum:
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
ut annuntient in Sion nomen Domini, et laudem ejus in Jerusalem:
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
in conveniendo populos in unum, et reges, ut serviant Domino.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Respondit ei in via virtutis suæ: Paucitatem dierum meorum nuntia mihi:
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
ne revoces me in dimidio dierum meorum, in generationem et generationem anni tui.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Initio tu, Domine, terram fundasti, et opera manuum tuarum sunt cæli.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Ipsi peribunt, tu autem permanes; et omnes sicut vestimentum veterascent. Et sicut opertorium mutabis eos, et mutabuntur;
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
tu autem idem ipse es, et anni tui non deficient.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Filii servorum tuorum habitabunt, et semen eorum in sæculum dirigetur.]

< Zabura 102 >