< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Preghiera di un afflitto che è stanco e sfoga dinanzi a Dio la sua angoscia. Signore, ascolta la mia preghiera, a te giunga il mio grido.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Non nascondermi il tuo volto; nel giorno della mia angoscia piega verso di me l'orecchio. Quando ti invoco: presto, rispondimi.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Si dissolvono in fumo i miei giorni e come brace ardono le mie ossa.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Il mio cuore abbattuto come erba inaridisce, dimentico di mangiare il mio pane.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Per il lungo mio gemere aderisce la mia pelle alle mie ossa.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Sono simile al pellicano del deserto, sono come un gufo tra le rovine.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Veglio e gemo come uccello solitario sopra un tetto.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Tutto il giorno mi insultano i miei nemici, furenti imprecano contro il mio nome.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Di cenere mi nutro come di pane, alla mia bevanda mescolo il pianto,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
davanti alla tua collera e al tuo sdegno, perché mi sollevi e mi scagli lontano.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
I miei giorni sono come ombra che declina, e io come erba inaridisco.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Ma tu, Signore, rimani in eterno, il tuo ricordo per ogni generazione.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Tu sorgerai, avrai pietà di Sion, perché è tempo di usarle misericordia: l'ora è giunta.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Poiché ai tuoi servi sono care le sue pietre e li muove a pietà la sua rovina.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
I popoli temeranno il nome del Signore e tutti i re della terra la tua gloria,
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
quando il Signore avrà ricostruito Sion e sarà apparso in tutto il suo splendore.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Egli si volge alla preghiera del misero e non disprezza la sua supplica.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Questo si scriva per la generazione futura e un popolo nuovo darà lode al Signore.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Il Signore si è affacciato dall'alto del suo santuario, dal cielo ha guardato la terra,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
per ascoltare il gemito del prigioniero, per liberare i condannati a morte;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
perché sia annunziato in Sion il nome del Signore e la sua lode in Gerusalemme,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
quando si aduneranno insieme i popoli e i regni per servire il Signore.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Ha fiaccato per via la mia forza, ha abbreviato i miei giorni.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Io dico: Mio Dio, non rapirmi a metà dei miei giorni; i tuoi anni durano per ogni generazione.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
In principio tu hai fondato la terra, i cieli sono opera delle tue mani.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Essi periranno, ma tu rimani, tutti si logorano come veste, come un abito tu li muterai ed essi passeranno.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Ma tu resti lo stesso e i tuoi anni non hanno fine.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
I figli dei tuoi servi avranno una dimora, resterà salda davanti a te la loro discendenza.

< Zabura 102 >