< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Ein Gebet des Elenden, wenn er schmachtet und seine Klage vor dem HERRN ausschüttet. O HERR, höre mein Gebet, und mein Schreien komme vor dich!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Verbirg dein Angesicht nicht vor mir am Tage meiner Not; neige dein Ohr zu mir; am Tage, da ich dich anrufe, erhöre mich eilends!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Denn meine Tage sind in Rauch aufgegangen, und meine Gebeine glühen wie ein Ofen.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Mein Herz ist geschlagen und verdorrt wie Gras; denn ich habe vergessen, mein Brot zu essen.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Vor lauter Seufzen kleben meine Knochen an meinem Fleisch.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Ich gleiche einer Rohrdommel in der Wüste, bin wie ein Käuzlein in den Ruinen;
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
ich wache und bin wie ein einsamer Vogel auf dem Dach.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Täglich schmähen mich meine Feinde, und die wider mich toben, schwören bei mir;
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
denn ich esse Asche wie Brot und mische meinen Trank mit Tränen
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
wegen deines Grimms und deines Zorns, daß du mich aufgehoben und hingeschleudert hast.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Meine Tage sind wie ein langgestreckter Schatten, und ich verdorre wie Gras.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Aber du, o HERR, bleibst ewig und dein Gedächtnis von einem Geschlecht zum andern.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Du wollest dich aufmachen und dich über Zion erbarmen; denn es ist Zeit, daß du ihr gnädig seiest, die Stunde ist gekommen!
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Denn deine Knechte lieben Zions Steine und trauern über ihren Schutt.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Dann werden die Heiden den Namen des HERRN fürchten und alle Könige auf Erden deine Herrlichkeit,
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
wenn der HERR Zion gebaut hat und erschienen ist in seiner Herrlichkeit,
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
wenn er sich zum Gebet der Heimatlosen gewendet und ihr Gebet nicht verachtet hat.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Das wird man aufschreiben für das spätere Geschlecht, und das Volk, das geschaffen werden soll, wird den HERRN loben,
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
daß er herabgeschaut hat von der Höhe seines Heiligtums, daß der HERR vom Himmel zur Erde geblickt hat,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
zu hören das Seufzen der Gefangenen und loszumachen die Kinder des Todes;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
auf daß sie den Namen des HERRN preisen zu Zion und sein Lob in Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
wenn die Völker sich versammeln allzumal und die Königreiche, dem HERRN zu dienen.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Er hat auf dem Wege meine Kraft gebeugt, meine Tage verkürzt.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Ich spreche: Mein Gott, nimm mich nicht weg in der Hälfte meiner Tage! Deine Jahre währen für und für.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Du hast vormals die Erde gegründet, und die Himmel sind deiner Hände Werk.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Sie werden vergehen, du aber bleibst; sie alle werden wie ein Kleid veralten, wie ein Gewand wirst du sie wechseln, und sie werden verschwinden.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Du aber bleibst, der du bist, und deine Jahre nehmen kein Ende!
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Die Kinder deiner Knechte werden bleiben, und ihr Same wird vor dir bestehen.