< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Ein Gebet des Elenden, so er betrübt ist und seine Klage vor dem HERRN ausschüttet. HERR, höre mein Gebet und laß mein Schreien zu dir kommen!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Verbirg dein Antlitz nicht vor mir in der Not, neige deine Ohren zu mir; wenn ich dich anrufe, so erhöre mich bald!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Denn meine Tage sind vergangen wie ein Rauch, und meine Gebeine sind verbrannt wie ein Brand.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Mein Herz ist geschlagen und verdorrt wie Gras, daß ich auch vergesse, mein Brot zu essen.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Mein Gebein klebt an meinem Fleisch vor Heulen und Seufzen.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Ich bin wie eine Rohrdommel in der Wüste; ich bin gleich wie ein Käuzlein in den verstörten Stätten.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Ich wache und bin wie ein einsamer Vogel auf dem Dache.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Täglich schmähen mich meine Feinde; und die mich verspotten, schwören bei mir.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Denn ich esse Asche wie Brot und mische meinen Trank mit Weinen
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
vor deinem Drohen und Zorn, daß du mich aufgehoben und zu Boden gestoßen hast.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Meine Tage sind dahin wie Schatten, und ich verdorre wie Gras.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Du aber, HERR, bleibst ewiglich und dein Gedächtnis für und für.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Du wollest dich aufmachen und über Zion erbarmen; denn es ist Zeit, daß du ihr gnädig seist, und die Stunde ist gekommen.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Denn deine Knechte wollten gerne, daß sie gebaut würde, und sähen gerne, daß ihre Steine und Kalk zugerichtet würden,
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
daß die Heiden den Namen des HERRN fürchten und alle Könige auf Erden dein Ehre,
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
daß der HERR Zion baut und erscheint in seiner Ehre.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Er wendet sich zum Gebet der Verlassenen und verschmäht ihr Gebet nicht.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Das werde geschrieben auf die Nachkommen; und das Volk, das geschaffen soll werden, wird den HERRN loben.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Denn er schaut von seiner heiligen Höhe, und der HERR sieht vom Himmel auf die Erde,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
daß er das Seufzen des Gefangenen höre und losmache die Kinder des Todes,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
auf daß sie zu Zion predigen den Namen des HERRN und sein Lob zu Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
wenn die Völker zusammenkommen und die Königreiche, dem HERRN zu dienen.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Er demütigt auf dem Wege meine Kraft; er verkürzt meine Tage.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Ich sage: Mein Gott, nimm mich nicht weg in der Hälfte meiner Tage! Deine Jahre währen für und für.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Du hast vormals die Erde gegründet, und die Himmel sind deiner Hände Werk.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Sie werden vergehen, aber du bleibest. Sie werden veralten wie ein Gewand; sie werden verwandelt wie ein Kleid, wenn du sie verwandeln wirst.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Du aber bleibest, wie du bist, und deine Jahre nehmen kein Ende.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Die Kinder deiner Knechte werden bleiben, und ihr Same wird vor dir gedeihen.

< Zabura 102 >