< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Gebet eines Elenden, wenn er schmachtet und vor Jahwe seine Klage ausschüttet. Jahwe, höre mein Gebet und laß mein Schreien vor dich kommen!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Verbirg dein Antlitz nicht vor mir, wenn mir angst ist! Neige dein Ohr zu mir; wenn ich rufe, eilends erhöre mich!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Denn meine Tage sind wie ein Rauch verschwunden, und meine Gebeine sind wie von Brand durchglüht.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Mein Herz ward versengt und verdorrte wie Gras; denn ich vergesse, mein Brot zu essen.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Von meinem lauten Stöhnen klebt mein Gebein an meinem Fleisch.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Ich gleiche dem Pelikan in der Wüste, bin wie ein Käuzlein in Ruinen.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Ich bin schlaflos und klage wie ein einsamer Vogel auf dem Dach.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Unaufhörlich lästern mich meine Feinde; die wider mich toben, schwören bei mir.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Denn ich esse Asche wie Brot und mische meinen Trank mit Thränen
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
wegen deines Grimms und deines Zorns; denn du hast mich emporgehoben und hingeschleudert.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Meine Tage gleichen einem langgestreckten Schatten, und ich verdorre wie Gras.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Du aber, Jahwe, thronst ewig, und dein Name währt durch alle Geschlechter.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Du wirst dich erheben, dich Zions zu erbarmen; denn es ist Zeit, sie zu begnadigen, denn die ihr bestimmte Frist ist eingetreten.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Denn deine Knechte hängen mit Liebe an ihren Steinen und jammern über ihren Schutt.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Und die Heiden werden den Namen Jahwes fürchten, und alle Könige der Erde deine Herrlichkeit,
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
weil Jahwe Zion wieder aufgebaut hat, erschienen ist in seiner Herrlichkeit,
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
sich dem Gebete des Nackten zugewendet und ihr Gebet nicht verschmäht hat.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Aufgeschrieben werde solches vom kommenden Geschlecht, und das Volk, das geschaffen werden soll, preise Jahwe,
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
daß er von seiner heiligen Höhe herabgeschaut, Jahwe vom Himmel auf die Erde geblickt hat,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
um das Seufzen des Gefangenen zu hören, die dem Tode Verfallenen loszumachen,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
daß man in Zion den Namen Jahwes verkünde und seinen Ruhm in Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
wenn sich die Völker allzumal versammeln und die Königreiche, um Jahwe zu dienen.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Er hat auf dem Wege meine Kraft gebeugt, meine Lebenstage verkürzt.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Ich spreche: Mein Gott, nimm mich nicht hinweg in der Hälfte meiner Tage, du, dessen Jahre durch alle Geschlechter währen.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Du hast vor Zeiten die Erde gegründet, und der Himmel ist deiner Hände Werk.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Sie werden vergehen, du aber bleibst: Sie werden insgesamt wie ein Gewand zerfallen; wie ein Kleid wirst du sie wechseln, und sie werden dahinfahren.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Du aber bist derselbe, und deine Jahre nehmen kein Ende.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Die Kinder deiner Knechte werden sicher wohnen, und ihre Nachkommen beständig vor dir bleiben.

< Zabura 102 >