< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Prière d’un malheureux, lorsqu’il est abattu et qu’il répand sa plainte devant l’Éternel. Éternel, écoute ma prière, Et que mon cri parvienne jusqu’à toi!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Ne me cache pas ta face au jour de ma détresse! Incline vers moi ton oreille quand je crie! Hâte-toi de m’exaucer!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Car mes jours s’évanouissent en fumée, Et mes os sont enflammés comme un tison.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Mon cœur est frappé et se dessèche comme l’herbe; J’oublie même de manger mon pain.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Mes gémissements sont tels Que mes os s’attachent à ma chair.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Je ressemble au pélican du désert, Je suis comme le chat-huant des ruines;
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Je n’ai plus de sommeil, et je suis Comme l’oiseau solitaire sur un toit.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Chaque jour mes ennemis m’outragent, Et c’est par moi que jurent mes adversaires en fureur.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Je mange la poussière au lieu de pain, Et je mêle des larmes à ma boisson,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
A cause de ta colère et de ta fureur; Car tu m’as soulevé et jeté au loin.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Mes jours sont comme l’ombre à son déclin, Et je me dessèche comme l’herbe.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Mais toi, Éternel! Tu règnes à perpétuité, Et ta mémoire dure de génération en génération.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Tu te lèveras, tu auras pitié de Sion; Car le temps d’avoir pitié d’elle, Le temps fixé est à son terme;
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Car tes serviteurs en aiment les pierres, Ils en chérissent la poussière.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Alors les nations craindront le nom de l’Éternel, Et tous les rois de la terre ta gloire.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Oui, l’Éternel rebâtira Sion, Il se montrera dans sa gloire.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Il est attentif à la prière du misérable, Il ne dédaigne pas sa prière.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Que cela soit écrit pour la génération future, Et que le peuple qui sera créé célèbre l’Éternel!
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
Car il regarde du lieu élevé de sa sainteté; Du haut des cieux l’Éternel regarde sur la terre,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
Pour écouter les gémissements des captifs, Pour délivrer ceux qui vont périr,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Afin qu’ils publient dans Sion le nom de l’Éternel, Et ses louanges dans Jérusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
Quand tous les peuples s’assembleront, Et tous les royaumes, pour servir l’Éternel.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Il a brisé ma force dans la route, Il a abrégé mes jours.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Je dis: Mon Dieu, ne m’enlève pas au milieu de mes jours, Toi, dont les années durent éternellement!
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Tu as anciennement fondé la terre, Et les cieux sont l’ouvrage de tes mains.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Ils périront, mais tu subsisteras; Ils s’useront tous comme un vêtement; Tu les changeras comme un habit, et ils seront changés.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
Mais toi, tu restes le même, Et tes années ne finiront point.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Les fils de tes serviteurs habiteront leur pays, Et leur postérité s’affermira devant toi.

< Zabura 102 >