< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
A prayer of the afflicted when he is faint and pours out his lament before Yahweh. Hear my prayer, Yahweh; hear my cry to you.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Do not hide your face from me in my time of trouble. Listen to me. When I call out to you, answer me quickly.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
For my days pass away like smoke, and my bones burn like fire.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
My heart is crushed, and I am like grass that has withered. I forget to eat any food.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
With my continual groaning, I have become very thin.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like a pelican of the wilderness; I have become like an owl in the ruins.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I lie awake like a solitary bird, alone on the housetop.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
My enemies taunt me all day long; those who mock me use my name in curses.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
I eat ashes like bread and mix my drink with tears.
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
Because of your raging anger, you have lifted me up to throw me down.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My days are like a shadow that fades, and I have withered like grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But you, Yahweh, live forever, and your fame is for all generations.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
You will rise up and have mercy on Zion. Now is the time to have mercy upon her; the appointed time has come.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For your servants hold her stones dear and feel compassion for the dust of her ruins.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
The nations will respect your name, Yahweh, and all the kings of the earth will honor your glory.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Yahweh will rebuild Zion and will appear in his glory.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
At that time, he will respond to the prayer of the destitute; he will not reject their prayer.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
This will be written for future generations, and a people not yet born will praise Yahweh.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
For he has looked down from the holy heights; from heaven Yahweh has viewed the earth,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
to hear the groaning of the prisoners, to release those who were condemned to death.
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Then men will proclaim the name of Yahweh in Zion and his praise in Jerusalem
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
when the peoples and kingdoms gather together to serve Yahweh.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
He has taken away my strength in the middle of life. He has shortened my days.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I said, “My God, do not take me away in the middle of life; you are here throughout all generations.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
In ancient times you set the earth in place; the heavens are the work of your hands.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They will perish, but you will remain; they will all grow old like a garment; like clothing, you will remove them, and they will disappear.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But you are the same, and your years will have no end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
The children of your servants will live on, and their descendants will live in your presence.”

< Zabura 102 >