< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
“A prayer of the afflicted, when in deep distress he poureth out his complaint before the Lord.” Hear my prayer, O LORD! And let my cry come unto thee!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Hide not thy face from me in the day of my trouble; Incline thine ear to me when I call! Answer me speedily!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
For my life is consumed like smoke, And my bones burn like a brand.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
My heart is smitten and withered like grass; Yea, I forget to eat my bread.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
By reason of my sighing, my bones cleave to my skin;
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like the pelican of the wilderness; I am like an owl amid ruins.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I am sleepless; I am like a solitary bird upon the house-top.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
All the day long my enemies reproach me; They who rage against me curse by me.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
For I eat ashes like bread, And mingle my drink with tears.
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
On account of thine indignation and thy wrath; For thou hast lifted me up and cast me down!
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My life is like a declining shadow, And I wither like grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But thou, O LORD! endurest for ever, And thy name from generation to generation!
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Thou wilt arise and have pity upon Zion, For the time to favor her, yea, the set time, is come.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For thy servants take pleasure in her stones; Yea, they have a regard for her dust.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Then shall the nations fear the name of Jehovah, And all the kings of the earth thy glory.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
For Jehovah will build up Zion; He will appear in his glory.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
He will regard the prayer of the destitute, And not despise their supplication.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
This shall be written for the generation to come, That the people to be born may praise Jehovah.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
For he looketh down from his holy height, From heaven doth he cast his eye upon the earth,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
To listen to the sighs of the prisoner. To release those that are doomed to death;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
That they may declare the name of Jehovah in Zion, And his praise in Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
When the nations are assembled together, And the kingdoms to serve Jehovah.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
He hath weakened my strength on the way, He hath shortened my days.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I say, O my God! take me not away in the midst of my days! Thy years endure through all generations.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Of old hast thou laid the foundations of the earth, And the heavens are the work of thy hands;
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They shall perish, but thou shalt endure; Yea, all of them shall wax old like a garment; As a vesture shalt thou change them, And they shall be changed;
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But thou art the same, And thy years have no end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
The children of thy servants shall dwell securely, And their posterity shall be established before thee.