< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
A prayer from someone who is suffering and is tired out, pouring out their troubles to the Lord. Lord please hear my prayer, my cry for help!
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Don't hide your face from me in my time of trouble! Turn and listen to me, and answer me quickly when I call.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
My life is disappearing like smoke; my body feels like it's on fire!
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
I'm like grass that's dried up, withered away—I even forget to eat!
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
All my groaning has worn me out; my bones show through my skin.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I'm like a desert owl, like a little owl among the ruins.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I can't sleep. I'm like a lonely bird on a rooftop.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
My enemies taunt me all day long. They mock me and swear at me.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Ashes are the food I eat; my tears drip into my drink,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
because of your anger and hostility, for you have picked me up and tossed me away.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My life is fading away like a shadow that lengthens—I'm withering away like grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But you, Lord, reign forever, your fame will last for all generations.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
You will take action and have pity on Jerusalem, for it's time to be kind to the city, the time has come.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For the people who follow you love its stones; they value even its dust!
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Then the nations will be in awe of who you are, Lord; all the kings of the earth will be in awe of your glory.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
For the Lord will rebuild Jerusalem; he will appear in glory.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
He will pay attention to the prayers of the homeless; he will not disregard their requests.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Let this be recorded for generations to come, so that people yet to be born may praise the Lord:
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
The Lord looked down from above, from the heights of his holy place; he looked down from heaven to the earth,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
to respond to the groans of prisoners, to set free the children of death.
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
As a result the wonderful nature of the Lord will be celebrated with praise in Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
when the people of many kingdoms gather together to worship the Lord.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
But as for me, he broke my health while I was still young, cutting my life short.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I cried out, “My God, don't take my life while I'm young! You are the one who lives forever.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Long ago you created the earth; you made the heavens.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They will come to an end, but you will not. They will all wear out, like clothes—you will change them, and throw them away.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But you are the one who always is; your years never come to an end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Our children will live with you, and our children's children will grow in your presence.”