< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
A Prayer of the man who is in trouble, when he is overcome, and puts his grief before the Lord. Give ear to my prayer, O Lord, and let my cry come to you.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Let not your face be veiled from me in the day of my trouble; give ear to me, and let my cry be answered quickly.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
My days are wasted like smoke, and my bones are burned up as in a fire.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
My heart is broken; it has become dry and dead like grass, so that I give no thought to food.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Because of the voice of my sorrow, my flesh is wasted to the bone.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
I am like a bird living by itself in the waste places; like the night-bird in a waste of sand.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
I keep watch like a bird by itself on the house-top.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
My haters say evil of me all day; those who are violent against me make use of my name as a curse.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
I have had dust for bread and my drink has been mixed with weeping:
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
Because of your passion and your wrath, for I have been lifted up and then made low by you.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
My days are like a shade which is stretched out; I am dry like the grass.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
But you, O Lord, are eternal; and your name will never come to an end.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
You will again get up and have mercy on Zion: for the time has come for her to be comforted.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
For your servants take pleasure in her stones, looking with love on her dust.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
So the nations will give honour to the name of the Lord, and all the kings of the earth will be in fear of his glory:
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
When the Lord has put up the walls of Zion, and has been been in his glory;
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
When he has given ear to the prayer of the poor, and has not put his request on one side.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
This will be put in writing for the coming generation, and the people of the future will give praise to the Lord.
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
For from his holy place the Lord has seen, looking down on the earth from heaven;
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
Hearing the cry of the prisoner, making free those for whom death is ordered;
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
So that they may give out the name of the Lord in Zion, and his praise in Jerusalem;
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
When the peoples are come together, and the kingdoms, to give worship to the Lord.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
He has taken my strength from me in the way; he has made short my days.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
I will say, O my God, take me not away before my time; your years go on through all generations:
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
In the past you put the earth on its base, and the heavens are the work of your hands.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
They will come to an end, but you will still go on; they all will become old like a coat, and like a robe they will be changed:
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
But you are the unchanging One, and your years will have no end.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
The children of your servants will have a safe resting-place, and their seed will be ever before you.