< Zabura 102 >

1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
Lamo mar ngʼat mawinjo marach kendo machiwo ywakne e nyim Jehova Nyasaye. Winj lamona, yaye Jehova Nyasaye; yie irwak lamona ma akwayigo kony.
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
Kik ipandna wangʼi sa ma chunya lit. Chikna iti; ka aluongi to dwoka mapiyo.
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Nimar ndalona rumo piyo ka iro; chokena rewni ka kit kendo maliet.
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
Chunya orewore kendo oner ka lum; wiya wil kata mana gi chamo chiemba.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Chur ma achurgo matek omiyo adhero alokora choke lilo.
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
Achalo gi tula mar bungu, achalo gi tula modak e gunda.
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
Asiko aneno anena, achalo gi winyo man kende ewi osuri.
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
Odiechiengʼ duto wasika kinya ka gijara; joma dhawona konyore gi nyinga kaka gir kwongʼruok.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Nimar achamo buch kendo kaka chiemba kendo ariwo mathna gi pi wangʼa,
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
nikech mirimbi maduongʼ, nimar isekawa mi iwita gichien.
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
Ndalona chalo gi tipo modhiambo; aner adwaro two ka lum.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
In to ibet e kom lochni nyaka chiengʼ, yaye Jehova Nyasaye; humbi osiko e tienge duto.
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
Ibiro aa malo mi ikech Sayun, nimar sa osechopo monego ongʼwonee; sa mochanne osechopo.
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
Nimar kitene beyo gi lala ne jotichni, kata mana buru madum kuome miyo ji keche.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Ogendini biro luoro nying Jehova Nyasaye, ruodhi duto mag piny biro luoro duongʼni.
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
Nimar Jehova Nyasaye biro gero Sayun kendo obiro thinyore e lela e duongʼne.
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
Obiro dwoko lamo mar ngʼama ok nyal kendo ok obi chayo lamogi.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
Wachni mondo ondik piny ne tiengʼ mabiro, mondo joma pok onywol opak Jehova Nyasaye:
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
“Jehova Nyasaye nongʼiyo piny gie kare maler man malo, nongʼiyo piny gie polo,
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
mondo owinj ywak joma otwe kendo ogony joma ongʼadnegi buch tho.”
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
Kuom mano nying Jehova Nyasaye ibiro hul e Sayun, ibiro pake e Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
ka joma odak e pinjeruodhi ochokore mondo olam Jehova Nyasaye.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Ka noyudo ngimana dhi maber to nomiyo tekona odok chien kendo nongʼado ngimana odoko machiek.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Omiyo ne awacho niya, “Kik ikaw ngimana, yaye Nyasacha, kapod an e chuny ngima; in to isiko ingima nyaka tienge duto.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Kar chakruok ne iketo mise mag piny, kendo polo bende gin tij lweti.
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
Gin to ginilal nono in to isiko manyaka chiengʼ; giduto giniti mana kaka law ti. Ibiro lokogi kaka iloko law kendo ibiro witgi.
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
In to isiko ichalri mana kaka in, kendo hiki ok norum.
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Nyithind jotichni biro dak buti machiegni; nyikwagi nodhi maber e nyimi.”

< Zabura 102 >