< Zabura 102 >
1 Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
(Bøn af en elendig, når hans Kraft svigter, og han udøser sin Klage for HERREN.) HERRE, lyt til min bøn, lad mit råb komme til dig,
2 Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
skjul dog ikke dit Åsyn for mig; den Dag jeg stedes i Nød, bøj da dit Øre til mig; når jeg kalder, så skynd dig og svar mig!
3 Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
Thi mine Dage svinder som Røg, mine Ledemod brænder som Ild;
4 Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
mit Hjerte er svedet og - visnet som Græs, thi jeg glemmer at spise mit Brød.
5 Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
Under min Stønnen klæber mine Ben til Huden;
6 Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
jeg ligner Ørkenens Pelikan, er blevet som Uglen på øde Steder;
7 Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
om Natten ligger jeg vågen og jamrer så ensom som Fugl på Taget;
8 Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
mine Fjender håner mig hele Dagen; de der spotter mig, sværger ved mig.
9 Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
Thi Støv er mit daglige Brød, jeg blander min Drik med Tårer
10 saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
over din Harme og Vrede, fordi du tog mig og slængte mig bort;
11 Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
mine Dage hælder som Skyggen, som Græsset visner jeg hen.
12 Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
Men du troner evindelig, HERRE, du ihukommes fra Slægt til Slægt;
13 Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
du vil rejse dig og forbarme dig over Zion, når Nådens Tid, når Timen er inde;
14 Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
thi dine Tjenere elsker dets Sten og ynkes over dets Grushobe.
15 Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
Og HERRENs Navn skal Folkene frygte, din Herlighed alle Jordens Konger;
16 Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
thi HERREN opbygger Zion, han lader sig se i sin Herlighed;
17 Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
han vender sig til de hjælpeløses Bøn, lader ej deres Bøn uænset.
18 Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
For Efterslægten skal det optegnes, af Folk, der skal fødes, skal prise HERREN;
19 “Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
thi han ser ned fra sin hellige Højsal, HERREN skuer ned fra Himmel til Jord
20 don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
for at høre de fangnes Stønnen og give de dødsdømte Frihed,
21 Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
at HERRENs Navn kan forkyndes i Zion, hans - Pris i Jerusalem,
22 sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
når Folkeslag og Riger til Hobe samles for at tjene HERREN.
23 Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
Han lammed min Kraft på Vejen, forkorted mit Liv.
24 Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
Jeg siger: Min Gud, tag mig ikke bort i Dagenes Hælvt! Dine År er fra Slægt til Slægt.
25 A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
Du grundfæsted fordum Jorden, Himlene er dine Hænders Værk;
26 Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
de falder, men du består, alle slides de op som en Klædning;
27 Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
som Klæder skifter du dem; de skiftes, men du er den samme, og dine År får aldrig Ende!
28 ’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”
Dine Tjeneres Børn fæster Bo, deres Sæd skal bestå for dit Åsyn.