< Zabura 101 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
مزمور داوود. ای خداوند، محبت و عدالت تو را می‌ستایم و با سرود تو را می‌پرستم.
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
مراقب خواهم بود تا راه درست و بی‌عیب را در پیش بگیرم. نزد من کِی خواهی آمد؟ در خانه خود، با دلی راست زندگی خواهم کرد.
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
هر چیز بد و ناپسند را از پیش چشم خود دور خواهم نمود. کردار افراد نادرست را دوست نخواهم داشت و در کارهایشان سهیم نخواهم شد.
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
نادرستی را از خود دور خواهم ساخت و با گناهکاران معاشرت نخواهم کرد.
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
کسی را که از دیگران بدگویی کند ساکت خواهم کرد؛ شخص مغرور و خودخواه را متحمل نخواهم شد.
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
من در پی اشخاص امین و خداشناس هستم تا آنها را به کاخ خود بیاورم. کسی که درستکار باشد، او را به کار خواهم گماشت.
7 Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
حیله‌گر به کاخ من راه نخواهد یافت و دروغگو نزد من نخواهد ماند.
8 Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.
هر روز عده‌ای از شریران را نابود خواهم کرد تا شهر خدا را از وجود همهٔ آنها پاک سازم.

< Zabura 101 >