< Zabura 101 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
Ngizahlabela ngomusa lesahlulelo; ngizahlabela kuwe, Nkosi.
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
Ngizaziphatha ngenhlakanipho ngendlela eqotho. Uzakuza nini kimi? Ngizahamba ngobuqotho benhliziyo yami phakathi kwendlu yami.
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
Kangiyikubeka phambi kwamehlo ami into embi. Ngiyakuzonda ukwenza kwabaphambukayo; kakuyikunamathela kimi.
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
Inhliziyo ephambeneyo izasuka kimi; kangiyikumazi omubi.
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
Ohleba umakhelwane wakhe ensitha, yena ngizamquma. Ophakeme ngamehlo, lolenhliziyo ezikhukhumezayo, yena kangiyikumvumela.
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
Amehlo ami azakuba kwabathembekileyo belizwe, ukuze bahlale lami. Ohamba endleleni eqotho, yena uzangikhonza.
7 Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
Owenza inkohliso kayikuhlala phakathi kwendlu yami; okhuluma amanga kayikuma phambi kwamehlo ami.
8 Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.
Insuku zonke ekuseni ngizabaquma bonke ababi belizwe, ukuze ngibaqume basuke emzini weNkosi bonke abenzi bobubi.

< Zabura 101 >