< Zabura 101 >

1 Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
Psaume de David. Je veux chanter la bonté et la justice; C'est toi, ô Éternel, que je célébrerai.
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
Je m'appliquerai à suivre la voie de l'intégrité. Quand viendras-tu à moi? Je donnerai l'exemple d'une conduite intègre. Au sein de ma famille.
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
Je chasserai de mon esprit toute pensée coupable. J'ai en horreur les actes d'iniquité: Ils n'ont aucun attrait pour moi.
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
Le coeur pervers s'éloignera de moi; Je ne connaîtrai point le mal.
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
J'anéantirai celui qui parle en secret contre son prochain. Je ne supporterai pas le regard hautain. Ni le coeur enflé d'orgueil.
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
J'aurai les yeux sur les fidèles du pays, Pour les faire demeurer avec moi. Celui qui marche dans l'intégrité, celui-là me servira.
7 Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
Celui qui use de tromperie n'habitera pas dans ma maison; Celui qui profère le mensonge Ne subsistera pas devant mes yeux.
8 Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.
Chaque matin, je détruirai tous les méchants du pays, Afin que tous les ouvriers d'iniquité Disparaissent de la cité de l'Éternel.

< Zabura 101 >