< Zabura 101 >
1 Ta Dawuda. Zabura ce. Zan rera wa ƙauna da adalcinka; gare ka, ya Ubangiji, zan rera yabo.
David’s. A Melody. Of lovingkindness and of justice, will I sing! Unto thee, O Yahweh, will I touch the strings!
2 Zan yi hankali ga yin rayuwa marar zargi, yaushe za ka zo gare ni? Zan bi da sha’anin gidana da zuciya marar abin zargi
I will behave myself wisely in a blameless way, When wilt thou come in unto me? I will walk to and fro in the blamelessness of my heart, —in the midst of my house:
3 Ba zan kafa a gaban idanuna 1 wani abu marar kyau ba. Na ƙi jinin ayyukan mutane marasa aminci; ba za su manne mini ba.
I will not set before mine eyes, a vile thing, —The doing of them who fall away, I hate, It shall not cleave unto me;
4 Mutane masu mugun zuciya za su nesa da ni; ba abin da zai haɗa ni da mugunta.
A perverse heart, shall depart from me, A maker of mischief, will I not acknowledge;
5 Duk wanda ya yi ɓatanci wa maƙwabcinsa a ɓoye shi za a kashe; duk mai renin wayo da mai girman kai, ba zan jure masa ba.
He that uttereth slander in secret against his friend, him, will I root out; One of lofty eyes, and of an ambitious heart, him shall I not be able to endure.
6 Idanuna za su kasance a kan amintattu a cikin ƙasar, don su zauna tare da ni; tafiyarsa ba ta da zargi zai yi mini hidima.
Mine eyes, shall be upon the faithful of the land, That they may dwell with me, —he that walketh in a blameless way, he, shall attend me.
7 Babu mai ruɗun da zai zauna a gidana; babu mai ƙaryan da zai tsaya a gabana.
There shall not dwell in the midst of my house, One who worketh deceit, —he that speaketh falsehoods, shall not be established before mine eyes;
8 Kowace safiya zan rufe bakunan dukan mugaye a ƙasar; zan yanke kowane mai aikata mugunta daga birnin Ubangiji.
Morning by morning, will I uproot, All the lawless ones of the land, That I may cut off, out of the city of Yahweh—All the workers of iniquity.