< Zabura 10 >

1 Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
Zakaj stojiš daleč stran, oh Gospod? Zakaj se skrivaš v časih stiske?
2 Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
Zlobni v svojem ponosu preganjajo revnega. Naj se ujamejo v naklepe, ki so si jih domislili.
3 Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
Kajti zlobni se baha z željo svojega srca in blagoslavlja pohlepnega, ki ga Gospod prezira.
4 Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
Zlobni zaradi ponosa svojega obličja ne bo povpraševal po Bogu. V vseh njegovih mislih ni Boga.
5 Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
Njegove poti so vedno boleče, tvoje sodbe so daleč zgoraj izven njegovega pogleda. Glede na vse njegove sovražnike on puha nanje.
6 Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
V svojem srcu je rekel: »Ne bom omajan, kajti nikoli ne bom v nadlogi.«
7 Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
Njegova usta so polna preklinjanj, prevare in sleparstva. Pod njegovim jezikom je vragolija in prazne reči.
8 Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
Sedi v skrivališčih vasi. Na skrivnih krajih mori nedolžnega. Njegove oči so na skrivaj naravnane zoper revnega.
9 Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
Na skrivnem preži kakor lev v svojem brlogu. Leži na preži, da ujame revnega. Revnega ujame, ko ga vleče v svojo mrežo.
10 Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
Klečeplazi in se ponižuje, da lahko revni pade po njegovih močnih.
11 Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
V svojem srcu je rekel: »Bog je pozabil. Skriva svoj obraz, tega nikoli ne bo videl.«
12 Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
Vstani, oh Gospod, oh Bog, dvigni svojo roko. Ne pozabi ponižnega.
13 Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
Zakaj zlobni zaničuje Boga? V svojem srcu je rekel: »Ti tega ne boš zahteval.«
14 Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
To si videl, kajti gledaš vragolijo in zlobnost, da to poplačaš s svojo roko. Revni se ti izroča, pomočnik si osirotelemu.
15 Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
Zlomi laket zlobnemu in zlemu človeku. Preiskuj njegovo zlobnost, dokler je ne najdeš več.
16 Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
Gospod je Kralj na veke vekov. Pogani so izginili iz njegove dežele.
17 Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
Gospod, slišal si hrepenenje ponižnih. Pripravil boš njihovo srce, svojemu ušesu boš povzročil, da sliši,
18 kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.
da razsodiš osirotelega in zatiranega, da človek iz zemlje ne more več zatirati.

< Zabura 10 >