< Zabura 10 >

1 Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
Por que você está longe, Yahweh? Por que você se esconde em tempos de dificuldade?
2 Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
Na arrogância, os malvados caçam os fracos. Eles estão presos nos esquemas que elaboram.
3 Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
Pois os ímpios se vangloriam dos anseios de seu coração. Ele abençoa os gananciosos e condena Yahweh.
4 Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
O ímpio, no orgulho de seu rosto, não tem espaço em seus pensamentos para Deus.
5 Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
Seus caminhos são sempre prósperos. Ele é arrogante, e suas leis estão longe de ser vistas por ele. Quanto a todos os seus adversários, ele zomba deles.
6 Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
Ele diz em seu coração: “Eu não serei abalado”. Por gerações não terei problemas”.
7 Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
Sua boca está cheia de palavrões, enganos e opressão. Debaixo de sua língua está a maldade e a iniquidade.
8 Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
Ele fica à espera perto das aldeias. De emboscadas, ele assassina os inocentes. Seus olhos estão em segredo contra os indefesos.
9 Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
Ele se esconde em segredo como um leão em sua emboscada. Ele fica à espera para pegar os indefesos. Ele pega os indefesos quando o atrai em sua rede.
10 Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
Os indefesos são esmagados. Eles caem. Eles caem sob suas forças.
11 Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
Ele diz em seu coração: “Deus esqueceu”. Ele esconde seu rosto. Ele nunca o verá”.
12 Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
Levanta-te, Yahweh! Deus, levante sua mão! Não se esqueça dos indefesos.
13 Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
Por que a pessoa perversa condena a Deus, e dizer em seu coração: “Deus não me chamará em conta”...
14 Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
Mas você vê problemas e tristezas. Você o considera para tomá-lo em suas mãos. Você ajuda a vítima e o órfão de pai.
15 Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
Quebre o braço dos ímpios. Quanto ao homem mau, procure sua perversidade até não encontrar nenhuma.
16 Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
Yahweh é Rei para todo o sempre! As nações perecerão fora de sua terra.
17 Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
Yahweh, você já ouviu o desejo dos humildes. Você vai preparar o coração deles. Você fará com que seu ouvido ouça,
18 kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.
para julgar os sem pai e os oprimidos, que o homem que é da terra não pode mais aterrorizar.

< Zabura 10 >