< Zabura 10 >

1 Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
Why stand you afar off, O LORD? why hide you yourself in times of trouble?
2 Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
The wicked in his pride does persecute the poor: let them be taken in the devices that they have imagined.
3 Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
For the wicked boasts of his heart’s desire, and blesses the covetous, whom the LORD abhors.
4 Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
The wicked, through the pride of his countenance, will not seek after God: God is not in all his thoughts.
5 Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
His ways are always grievous; your judgments are far above out of his sight: as for all his enemies, he puffs at them.
6 Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
He has said in his heart, I shall not be moved: for I shall never be in adversity.
7 Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
His mouth is full of cursing and deceit and fraud: under his tongue is mischief and vanity.
8 Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
He sits in the lurking places of the villages: in the secret places does he murder the innocent: his eyes are privately set against the poor.
9 Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
He lies in wait secretly as a lion in his den: he lies in wait to catch the poor: he does catch the poor, when he draws him into his net.
10 Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
He crouches, and humbles himself, that the poor may fall by his strong ones.
11 Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
He has said in his heart, God has forgotten: he hides his face; he will never see it.
12 Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
Arise, O LORD; O God, lift up your hand: forget not the humble.
13 Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
Why does the wicked scorn God? he has said in his heart, You will not require it.
14 Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
You have seen it; for you behold mischief and spite, to requite it with your hand: the poor commits himself to you; you are the helper of the fatherless.
15 Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
Break you the arm of the wicked and the evil man: seek out his wickedness till you find none.
16 Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
The LORD is King for ever and ever: the heathen are perished out of his land.
17 Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
LORD, you have heard the desire of the humble: you will prepare their heart, you will cause your ear to hear:
18 kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.
To judge the fatherless and the oppressed, that the man of the earth may no more oppress.

< Zabura 10 >