< Zabura 10 >

1 Don me, ya Ubangiji, kake tsaya can da nesa? Me ya sa kake ɓoye kanka a lokutan wahala?
LAMED Zašto, Jahve, stojiš daleko, zašto se skrivaš u dane tjeskobe?
2 Cikin fariyarsa mugun mutum yakan cuci marasa ƙarfi, waɗanda yake kama cikin makircin da ya shirya.
Obijesni bezbožnik jadnika goni, u zamke ga hvata koje mu postavi.
3 Yakan yi taƙama da ƙulle-ƙullen zuciyarsa; yana albarkaci mai haɗama yana kuma ƙin Ubangiji.
Bezbožnik se pohlepom hvali, NUN lakomac psuje i Jahvu prezire.
4 Cikin ɗaga kai mutum ba ya neman Allah; cikin tunaninsa ba ya ba da wata dama saboda Allah.
Bezbožnik zbori u obijesti svojoj: “Ne, istrage nema! TÓa ni Boga nema!” I u tome sva mu je misao.
5 Hanyoyinsa kullum sukan yi nasara; yana da girman kai kuma dokokinka suna nesa da shi; yakan yi wa dukan abokan gābansa duban reni.
Puti su mu svagda uspješni, na sudove tvoje on i ne misli, sve protivnike svoje prezire.
6 Yakan ce wa kansa, “Ba abin da zai girgiza ni; kullum zan yi murna ba zan taɓa shiga wahala ba.”
U srcu veli: “Neću posrnuti! Ni u kojem koljenu neću biti nesretan.”
7 Bakinsa ya cika da zage-zage da ƙarairayi da kuma barazana; wahala da mugunta suna a ƙarƙashin harshensa.
PE Usta mu puna kletve, lukavstva i prijevare, pod jezikom njegovim muka i nesreća.
8 Yakan yi kwanto kusa da ƙauyuka; daga kwanton yakan kashe marar laifi. Yana kallon waɗanda za su shiga hannunsa a ɓoye.
U zasjedi čuči pokraj ograda, potajno ubija nevina, AJIN očima siromaha vreba.
9 Yakan yi kwanto a ɓoye kamar zaki. Yakan yi kwanto don yă kama marasa ƙarfi; yakan kama marasa ƙarfi yă ja su cikin ragarsa.
U zaklonu sjedi k'o lav u pećini, vreba da opljačka jadnika i da ga povuče u mrežu.
10 Yakan ragargaza waɗanda suka shiga hannu, su fāɗi; sukan fāɗi a ƙarƙashin ƙarfinsa.
Pritajen čuči na zemlji, od nasilja mu siromasi padaju.
11 Yakan ce wa kansa, “Ai, Allah ya manta; ya rufe fuskarsa ba ya gani.”
U srcu svome veli: “ZÓaboravi Gospod, odvrati lice i nikoga ne vidi!”
12 Ka tashi, Ubangiji! Ka hukunta miyagu, ya Allah. Kada ka manta da marasa ƙarfi.
KOF Ustani, Gospode Bože, podigni ruku, ne zaboravi siromaha.
13 Don me mugun mutum zai ƙi Allah? Don me yakan ce wa kansa, “Allah ba zai nemi hakki daga gare ni ba”?
Zašto da bezbožnik prezire Boga, zašto da kaže u srcu: “Neće kazniti!”
14 Amma kai, ya Allah, kana gani wahala da baƙin ciki; kana lura da yadda suke ɗaukansu a hannu. Marar taimako kan danƙa kansa gare ka; kai ne mai taimakon marayu
REŠ Jer ti vidiš, gledaš jad i nevolju, u ruci je mjeriš. Siromah se tebi predaje, ubogu ti si pomoć!
15 Ka karye hannun mugaye da kuma mugun mutum; ka nemi hakki daga gare shi saboda muguntar da ba za a gane ba.
ŠIN Pakosnu grešniku satri mišicu, kazni mu pakost da je više ne bude!
16 Ubangiji Sarkin har abada abadin ne; al’ummai za su hallaka daga ƙasarsa.
Jahve je kralj u vijeke vjekova, iz zemlje njegove nestat će pogana.
17 Kakan ji, ya Ubangiji sha’awar mai shan wahala; kakan ƙarfafa su, ka kuma saurari kukansu,
TAU Počuj, o Jahve, čežnju siromašnih, okrijepi im srce, uho prikloni:
18 kana kāre marayu da waɗanda aka danne, domin mutum, wanda yake na duniya kada ƙara haddasa wata razana.
da zaštitiš pravo ubogih i tlačenih, da straha više ne zadaje čovjek zemljanÄi.

< Zabura 10 >