< Zabura 1 >
1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
Bemaventurado o varão que não anda no conselho dos impios, nem está no caminho dos peccadores, nem se assenta no assento dos escarnecedores.
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
Antes tem o seu prazer na lei do Senhor, e na sua lei medita de dia e de noite.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
Pois será como a arvore plantada junto a ribeiros de aguas, que dá o seu fructo no seu tempo; as suas folhas não cairão, e tudo quanto fizer prosperará.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
Não são assim os impios: mas são como a moinha que o vento espalha.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Pelo que os impios não subsistirão no juizo, nem os peccadores na congregação dos justos.
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
Porque o Senhor conhece o caminho dos justos; porém o caminho dos impios perecerá.