< Zabura 1 >

1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
[God] is pleased with those who do not do what [MET] wicked people advise them to do, and who do not imitate the behavior of [MET] sinful people, and who do not join in with people who (ridicule/sneer at) [God].
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
Those whom God is pleased with delight in doing the things that he has instructed/taught us to do. They read and think about Yahweh’s requirements, day and night.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
They [constantly produce/do things that please God] just like fruit trees that have been planted along the banks of a stream produce fruit at the right time every year. [Like] trees that never wither, they succeed in everything that they do.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
But wicked people are not like that! Wicked people are [as worthless as] chaff that is blown away by the wind.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Therefore, wicked people (will not be acquitted/will be condemned) [LIT] when [God] judges people, and furthermore, sinful people will not even be present when [God] gathers righteous people together,
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
because he guides and protects righteous people, but the path that the wicked walk on leads them to where they will be destroyed/punished [by God forever].

< Zabura 1 >