< Zabura 1 >

1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
“BOOK I” Happy the man who walketh not in the counsel of the unrighteous, Nor standeth in the way of sinners, Nor sitteth in the seat of scoffers;
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
But whose delight is in the law of the LORD, And who meditateth on his precepts day and night.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
He is like a tree planted by streams of water, That bringeth forth its fruit in its season, Whose leaves also do not wither: All that he doeth shall prosper.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
Not so the unrighteous; They are like chaff, which the wind driveth away.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Therefore the wicked shall not stand in judgment, Nor sinners in the assembly of the just.
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
For the LORD knoweth the way of the righteous, But the way of the wicked leadeth to ruin.

< Zabura 1 >