< Karin Magana 1 >
1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Los proverbios de Salomón, hijo de David, rey de Israel:
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Para entender sabiduría y castigo: para entender las razones prudentes:
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Para recibir el castigo de prudencia, justicia, y juicio, y equidad:
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Para dar a los simples astucia, y a los mozos inteligencia y consejo.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Oirá el sabio y aumentará la doctrina; y el entendido adquirirá consejo.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Para entender parábola y declaración, palabras de sabios, y sus dichos oscuros.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
El principio de la sabiduría es el temor de Jehová: los insensatos despreciaron la sabiduría y la instrucción.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Oye, hijo mío, el castigo de tu padre, y no deseches la ley de tu madre:
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Porque aumento de gracia serán a tu cabeza, y collares a tu cuello.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Hijo mío, si los pecadores te quisieren engañar, no consientas.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Si dijeren: Ven con nosotros, espiemos a la sangre: asechemos al inocente sin razón:
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
Tragarlos hemos como el sepulcro, vivos; y enteros, como los que caen en sima: (Sheol )
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Hallaremos riquezas de todas suertes: henchiremos nuestras casas de despojos:
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Echa tu suerte entre nosotros: tengamos todos una bolsa:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Hijo mío, no andes en camino con ellos: aparta tu pie de sus veredas:
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Porque sus pies correrán al mal; e irán presurosos a derramar sangre.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Porque en vano se tenderá la red delante de los ojos de toda ave.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Mas ellos a su sangre espían, y a sus almas asechan.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Tales son las sendas de todo codicioso de codicia, la cual prenderá el alma de sus poseedores.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
La sabiduría clama de fuera: en las plazas da su voz:
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
En las encrucijadas de los murmullos de gente clama: en las entradas de las puertas de la ciudad dice sus razones:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
¿Hasta cuándo, o! simples, amaréis la simpleza, y los burladores desearán el burlar, y los insensatos aborrecerán la ciencia?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Volvéos a mi reprensión: he aquí que yo os derramaré mi espíritu, y os haré saber mis palabras.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Por cuanto llamé, y no quisisteis: extendí mi mano, y no hubo quien escuchase:
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Y desechasteis todo consejo mío, y no quisisteis mi reprensión:
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
También yo me reiré en vuestra calamidad; y me burlaré cuando os viniere lo que teméis.
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Cuando viniere, como una destrucción, lo que teméis; y vuestra calamidad viniere como un torbellino: cuando viniere sobre vosotros tribulación y angustia:
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Entonces me llamarán, y no responderé: buscarme han de mañana, y no me hallarán:
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Por cuanto aborrecieron la sabiduría; y no escogieron el temor de Jehová:
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Ni quisieron mi consejo; y menospreciaron toda reprensión mía.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Comerán pues del fruto de su camino; y de sus consejos se hartarán.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Porque el reposo de los ignorantes los matará; y la prosperidad de los insensatos los echará a perder.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Mas el que me oyere, habitará confiadamente; y vivirá reposado de temor de mal.