< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Provérbios de Salomão, filho de David, rei de Israel;
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Para se conhecer a sabedoria e a instrução; para se entenderem as palavras da prudência;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Para se receber a instrução do entendimento, a justiça, o juízo, e a equidade;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
Para dar aos símplice prudência, e aos moços conhecimento e bom siso;
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Para o sábio ouvir e crescer em doutrina, e o entendido adquirir sábios conselhos;
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
Para entender provérbios e a sua declaração: como também as palavras dos sábios, e as suas adivinhações.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
O temor do Senhor é o princípio da ciência: os loucos desprezam a sabedoria e a instrução.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Filho meu, ouve a instrução de teu pai, e não deixes a doutrina de tua mãe.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Porque diadema de graça serão para a tua cabeça, e colares para o teu pescoço.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Filho meu, se os pecadores te atraírem com afagos, não consintas.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Se disserem: Vem conosco; espiemos o sangue; espreitemos o inocente sem razão;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Traguemo-los vivos, como a sepultura; e inteiros, como os que descem à cova; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Acharemos toda a sorte de fazenda preciosa; encheremos as nossas casas de despojos;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Lança a tua sorte entre nós; teremos todos uma só bolsa.
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
Filho meu, não te ponhas a caminho com eles: desvia o pé das suas veredas;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Porque os seus pés correm para o mal, e se apressam a derramar sangue.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Na verdade debalde se estende a rede perante os olhos de toda a sorte de aves.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
E estes armam ciladas contra o seu próprio sangue; e as suas próprias vidas espreitam.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Assim são as veredas de todo aquele que usa de avareza: ela prenderá a alma de seus amos.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
A suprema sabedoria altamente clama de fora: pelas ruas levanta a sua voz.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
Nas encruzilhadas, em que há tumultos, clama: às entradas das portas, na cidade profere as suas palavras.
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Até quando, ó símplices, amareis a simplicidade? e vós, escarnecedores, desejareis o escarneio? e vós, loucos, aborrecereis o conhecimento?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Tornai-vos à minha repreensão: eis que abundantemente vos derramarei de meu espírito e vos farei saber as minhas palavras.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Porquanto clamei, e vós recusastes; estendi a minha mão, e não houve quem desse atenção;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
Mas rejeitastes todo o meu conselho, e não quizestes a minha repreensão.
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Também eu me rirei na vossa perdição, e zombarei, vindo o vosso temor;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
Vindo como a assolação o vosso temor, e vindo a vossa perdição como uma tormenta, sobrevindo-vos aperto e angústia.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Então a mim clamarão, porém eu não responderei; de madrugada me buscarão, porém não me acharão.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Porquanto aborreceram o conhecimento; e não elegeram o temor do Senhor;
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Não consentiram ao meu conselho e desprezaram toda a minha repreensão.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Assim que comerão do fruto do seu caminho, e fartar-se-ão dos seus próprios conselhos.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Porque o desvio dos símplices os matará, e a prosperidade dos loucos os destruirá.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Porém o que me der ouvidos habitará seguramente, e estará descançado do temor do mal

< Karin Magana 1 >