< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Dies sind die Sprüche Salomos, des Königs in Israel, des Sohnes Davids,
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
zu lernen Weisheit und Zucht, Verstand
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
Klugheit, Gerechtigkeit, Recht und Schlecht;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
daß die Unverständigen klug und die Jünglinge vernünftig und vorsichtig werden.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Wer weise ist der hört zu und bessert sich; wer verständig ist, der läßt sich raten,
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
daß er verstehe die Sprüche und ihre Deutung, die Lehre der Weisen und ihre Beispiele.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
Des HERRN Furcht ist Anfang der Erkenntnis. Die Ruchlosen verachten Weisheit und Zucht.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Mein Kind, gehorche der Zucht deines Vaters und verlaß nicht das Gebot deiner Mutter.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
Denn solches ist ein schöner Schmuck deinem Haupt und eine Kette an deinem Hals.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Mein Kind, wenn dich die bösen Buben locken, so folge nicht.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Wenn sie sagen: “Gehe mit uns! wir wollen auf Blut lauern und den Unschuldigen ohne Ursache nachstellen;
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
wir wollen sie lebendig verschlingen wie die Hölle und die Frommen wie die, so hinunter in die Grube fahren; (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
wir wollen großes Gut finden; wir wollen unsre Häuser mit Raub füllen;
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
wage es mit uns! es soll unser aller ein Beutel sein”:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
mein Kind, wandle den Weg nicht mit ihnen; wehre deinem Fuß vor ihrem Pfad.
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
Denn ihr Füße laufen zum Bösen und eilen, Blut zu vergießen.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Denn es ist vergeblich, das Netz auswerfen vor den Augen der Vögel.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Sie aber lauern auf ihr eigen Blut und stellen sich selbst nach dem Leben.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Also geht es allen, die nach Gewinn geizen, daß ihr Geiz ihnen das Leben nimmt.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Die Weisheit klagt draußen und läßt sich hören auf den Gassen;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
sie ruft in dem Eingang des Tores, vorn unter dem Volk; sie redet ihre Worte in der Stadt:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Wie lange wollt ihr Unverständigen unverständig sein und die Spötter Lust zu Spötterei und die Ruchlosen die Lehre hassen?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Kehret euch zu meiner Strafe. Siehe, ich will euch heraussagen meinen Geist und euch meine Worte kundtun.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Weil ich denn rufe, und ihr weigert euch, ich recke meine Hand aus, und niemand achtet darauf,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
und laßt fahren allen meinen Rat und wollt meine Strafe nicht:
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
so will ich auch lachen in eurem Unglück und eurer spotten, wenn da kommt, was ihr fürchtet,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
wenn über euch kommt wie ein Sturm, was ihr fürchtet, und euer Unglück als ein Wetter, wenn über euch Angst und Not kommt.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Dann werden sie nach mir rufen, aber ich werde nicht antworten; sie werden mich suchen, und nicht finden.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Darum, daß sie haßten die Lehre und wollten des HERRN Furcht nicht haben,
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
wollten meinen Rat nicht und lästerten alle meine Strafe:
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
so sollen sie essen von den Früchten ihres Wesens und ihres Rats satt werden.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
Was die Unverständigen gelüstet, tötet sie, und der Ruchlosen Glück bringt sie um.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Wer aber mir gehorcht, wird sicher bleiben und genug haben und kein Unglück fürchten.

< Karin Magana 1 >