< Karin Magana 1 >
1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
[the] proverbs of Solomon [the] son of David [the] king of Israel.
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
To learn wisdom and discipline to teach words of understanding.
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
To receive correction of insight righteousness and justice and uprightness.
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
To give to naive people prudence to a youth knowledge and discretion.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
Let him listen a prudent [one] and let him increase insight and a discerning [one] wise directions let him get.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
To understand a proverb and an enigma [the] words of learned ones and parables their.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
[the] fear of Yahweh [is the] beginning of knowledge wisdom and discipline fools they despise.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Listen to O son my [the] correction of father your and may not you reject [the] instruction of mother your.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
For - [will be] a wreath of favor they for head your and necklaces for neck your.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
O son my if they will entice you sinners may not you be willing.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
If they will say come! with us let us lie in wait for blood let us lie hidden for an innocent [one] without cause.
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol )
Let us engulf them like Sheol alive and complete like [those who] go down of [the] pit. (Sheol )
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
All wealth prized we will find we will fill houses our plunder.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Lot your you will cast in midst of us a bag one it will belong to all of us.
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
O son my may not you walk in [the] way with them restrain foot your from pathway their.
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
For feet their to evil they run and they may make haste to shed blood.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
For in vain [is] spread out the net in [the] eyes of every owner of a wing.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
And they for own blood their they lie in wait they lie hidden for own life their.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
[are] thus [the] paths of Every [one who] gains unjustly unjust gain [the] life of owners its it will take.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Wisdom in the street it cries aloud in the open places she gives voice her.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
At [the] top of noisy [places] she calls out at [the] entrances of [the] gates in the city sayings her she utters.
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Until when? - O naive people will you love naivete and mockers mockery do they delight in? themselves and fools will they hate? knowledge.
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
You will turn back to rebuke my here! I will pour out to you spirit my let me declare words my you.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Because I called and you refused I offered hand my and there not [was] an attentive [one].
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
And you ignored all advice my and rebuke my not you yielded to.
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Also I at calamity your I will laugh I will mock when comes dread your.
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
When comes (like devastation *Q(K)*) dread your and calamity your like a storm-wind it will arrive when comes on you trouble and distress.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Then they will call to me and not I will answer they will earnestly seek me and not they will find me.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
Because for they hated knowledge and [the] fear of Yahweh not they chose.
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
Not they yielded to advice my they spurned all rebuke my.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
So they may eat from [the] fruit of way their and from own schemes their they will be surfeited.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
For [the] waywardness of naive people it will ruin them and [the] ease of fools it will destroy them.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
And [one who] listens to me he will dwell security and he will be at ease from dread of trouble.