< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
THE proverbs of Solomon the son of David, king of Israel;
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
To know wisdom and instruction; to perceive the words of understanding;
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
To receive the instruction of wisdom, justice, and judgment, and equity;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
To give subtilty to the simple, to the young man knowledge and discretion.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
A wise man will hear, and will increase learning; and a man of understanding shall attain unto wise counsels:
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
To understand a proverb, and the interpretation; the words of the wise, and their dark sayings.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
The fear of the Lord is the beginning of knowledge: but fools despise wisdom and instruction.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
My son, hear the instruction of thy father, and forsake not the law of thy mother:
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
For they shall be an ornament of grace unto thy head, and chains about thy neck.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
My son, if sinners entice thee, consent thou not.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
If they say, Come with us, let us lay wait for blood, let us lurk privily for the innocent without cause:
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Let us swallow them up alive as the grave; and whole, as those that go down into the pit: (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
We shall find all precious substance, we shall fill our houses with spoil:
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Cast in thy lot among us; let us all have one purse:
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
My son, walk not thou in the way with them; refrain thy foot from their path:
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
For their feet run to evil, and make haste to shed blood.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Surely in vain the net is spread in the sight of any bird.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
And they lay wait for their own blood; they lurk privily for their own lives.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
So are the ways of every one that is greedy of gain; which taketh away the life of the owners thereof.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Wisdom crieth without; she uttereth her voice in the streets:
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
She crieth in the chief place of concourse, in the openings of the gates: in the city she uttereth her words, saying,
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
How long, ye simple ones, will ye love simplicity? and the scorners delight in their scorning, and fools hate knowledge?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Turn you at my reproof: behold, I will pour out my spirit unto you, I will make known my words unto you.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Because I have called, and ye refused; I have stretched out my hand, and no man regarded;
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
But ye have set at nought all my counsel, and would none of my reproof:
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
I also will laugh at your calamity; I will mock when your fear cometh;
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
When your fear cometh as desolation, and your destruction cometh as a whirlwind; when distress and anguish cometh upon you.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Then shall they call upon me, but I will not answer; they shall seek me early, but they shall not find me:
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
For that they hated knowledge, and did not choose the fear of the Lord:
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
They would none of my counsel: they despised all my reproof.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Therefore shall they eat of the fruit of their own way, and be filled with their own devices.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
For the turning away of the simple shall slay them, and the prosperity of fools shall destroy them.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
But whoso hearkeneth unto me shall dwell safely, and shall be quiet from fear of evil.

< Karin Magana 1 >