< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
The parables of Solomon, son of David, king of Israel,
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
in order to know wisdom and discipline,
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
to understand words of prudence, and to accept the instruction of doctrine, justice and judgment, and equity,
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
so as to give discernment to little ones, knowledge and understanding to adolescents.
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
By listening, the wise shall become wiser and the intelligent shall possess governments.
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
He shall turn his soul to a parable and to its interpretation, to the words of the wise and their enigmas.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
The fear of the Lord is the beginning of wisdom. The foolish despise wisdom as well as doctrine.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Listen, my son, to the discipline of your father, and forsake not the law of your mother,
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
so that grace may be added to your head and a collar to your neck.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
My son, if sinners should entice you, do not consent to them.
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
If they should say: “Come with us. We will lie in wait for blood. We will lay traps against the innocent, without cause.
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Let us swallow him alive, like Hell, and whole, like one descending into the pit. (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
We will discover every precious substance. We will fill our houses with spoils.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Cast your lot with us. One purse will be for us all.”
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
My son, do not walk with them. Preclude your feet from their paths.
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
For their feet rush to evil, and they hurry to shed blood.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
But a net is thrown in vain before the eyes of those who have wings.
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
Likewise, they lie in ambush against their own blood, and they undertake deceits against their own souls.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Thus, the ways of all those who are greedy seize the souls of those who possess.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Wisdom forewarns far and wide; she bestows her voice in the streets.
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
She cries out at the head of crowds; at the entrance of the gates of the city, she offers her words, saying:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
“Little ones, how long will you choose to be childish, and how long will the foolish desire what is harmful to themselves, and how long will the imprudent hate knowledge?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Be converted by my correction. Lo, I will offer my spirit to you, and I will reveal my words to you.
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
For I called, and you refused. I extended my hand, and there was no one who watched.
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
You have despised all my counsels, and you have neglected my rebukes.
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
Similarly, I will ridicule you at your demise, and I will mock you, when that which you feared shall overcome you.
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
When sudden calamity rushes upon you, and your demise advances like a tempest, when tribulation and anguish overcome you,
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
then they will call to me, and I will not heed, they will arise in the morning, and not find me.
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
For they held hatred for discipline, and they would not accept the fear of the Lord;
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
they would not consent to my counsel, but they detracted from all of my corrections.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Therefore, they shall eat the fruit of their way, and they shall have their fill of their own counsels.
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
The loathing of the little ones shall destroy them, and the prosperity of the foolish shall perish them.
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
But whoever will listen to me shall rest without terror, and shall have full enjoyment of abundance, without fear of evils.”

< Karin Magana 1 >