< Karin Magana 1 >

1 Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
Ordsprog af Salomo, Davids Søn, Israels Konge.
2 Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
Af dem skal man lære Visdom forstandig Tale,
3 don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
tage mod Tugt, som gør klog, mod Retfærdighed, Ret og Retsind;
4 don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
de skal give tankeløse Klogskab, ungdommen Kundskab og Kløgt;
5 bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
den vise høre og øge sin Viden, den forstandige vinde sig Levekunst;
6 don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
de skal lære at tyde Ordsprog og Billeder, de vises Ord og Gåder.
7 Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
HERRENs Frygt er Kundskabs begyndelse, Dårer ringeagter Visdom og Tugt.
8 Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
Hør, min Søn, på din Faders Tugt, opgiv ikke din Moders Belæring.
9 Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
thi begge er en yndig Krans til dit Hoved og Kæder til din Hals.
10 Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
Min Søn, sig nej, når Syndere lokker!
11 In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
Siger de: "Kom med, lad os lure på den fromme, lægge Baghold for sagesløs, skyldfri Mand!
12 mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
Som Dødsriget sluger vi dem levende, med Hud og Hår, som for de i Graven. (Sheol h7585)
13 za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
Vi vinder os Gods og Guld, vi fylder vore Huse med Rov.
14 ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
Gør fælles Sag med os; vi har alle fælles Pung!"
15 ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
- min Søn, gå da ikke med dem, hold din Fod fra deres Sti;
16 gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
thi deres Fødder løber efter ondt, de haster for at udgyde Blod.
17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
Thi det er unyttigt at udspænde Garnet for alle Fugles Øjne;
18 Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
de lurer på eget Blod, lægger Baghold for eget Liv.
19 Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
Så går det enhver, der attrår Rov, det tager sin Herres Liv.
20 Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
Visdommen råber på Gaden, på Torvene løfter den Røsten;
21 tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
oppe på Murene kalder den, tager til Orde i Byen ved Portindgangene:
22 “Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
Hvor længe vil I tankeløse elske Tankeløshed, Spotterne finde deres Glæde i Spot og Dårerne hade kundskab?
23 Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
Vend eder til min Revselse! Se, jeg lader min Ånd udvælde for eder, jeg kundgør eder mine Ord:
24 Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
Fordi jeg råbte og I stod imod, jeg vinked og ingen ænsed det,
25 da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
men I lod hånt om alt mit Råd og tog ikke min Revselse til jer,
26 Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
derfor ler jeg ved eders Ulykke, spotter, når det, I frygter, kommer,
27 sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
når det, I frygter, kommer som Uvejr, når eders Ulykke kommer som Storm, når Trængsel og Nød kommer over jer.
28 “Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
Da svarer jeg ej, når de kalder, de søger mig uden at finde,
29 Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
fordi de hadede Kundskab og ikke valgte HERRENs Frygt;
30 da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
mit Råd tog de ikke til sig, men lod hånt om al min Revselse.
31 za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
Frugt af deres Færd skal de nyde og mættes med egne Råd;
32 Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
thi tankeløses Egensind bliver deres Død, Tåbers Sorgløshed bliver deres Undergang;
33 amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
men den, der adlyder mig, bor trygt, sikret mod Ulykkens Rædsel.

< Karin Magana 1 >