< Karin Magana 9 >
1 Hikima ta gina gidanta; ta yi ginshiƙansa bakwai.
Bilgelik kendi evini yaptı, Yedi direğini yonttu.
2 Ta shirya abincinta gauraye da ruwan inabinta; ta kuma shirya teburinta.
Hayvanlarını kesti, Şarabını hazırlayıp sofrasını kurdu.
3 Ta aiki bayinta mata, tana kuma kira daga wurare masu tsayi na birnin.
Kentin en yüksek noktalarına gönderdiği Hizmetçileri aracılığıyla herkesi çağırıyor:
4 “Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo nan ciki!” Tana faɗa wa marasa hankali.
“Kim safsa buraya gelsin” diyor. Sağduyudan yoksun olanlara da, “Gelin, yiyeceklerimi yiyin, Hazırladığım şaraptan için” diyor.
5 “Ku zo, ku ci abincina da ruwan inabin da na gauraye.
6 Ku bar hanyoyinku marasa hankali za ku kuwa rayu; yi tafiya a hanyar fahimi.
“Saflığı bırakın da yaşayın, Aklın yolunu izleyin.
7 “Duk wanda ya yi wa mai ba’a gyara yana gayyatar zagi duk wanda ya tsawata wa mugu yakan gamu da cin mutunci.
“Alaycıyı paylayan aşağılanmayı hak eder, Kötü kişiyi azarlayan hakarete uğrar.
8 Kada ka tsawata wa masu ba’a gama za su ƙi ka; ka tsawata wa mai hikima zai kuwa ƙaunace ka.
Alaycıyı azarlama, yoksa senden nefret eder. Bilge kişiyi azarlarsan, seni sever.
9 Ka koya wa mai hikima zai kuwa ƙara hikima; ka koya wa mai adalci zai kuwa ƙara koyonsa.
Bilge kişiyi eğitirsen Daha bilge olur, Doğru kişiye öğretirsen bilgisini artırır.
10 “Tsoron Ubangiji shi ne mafarin hikima, sanin Mai Tsarki kuwa fahimi ne.
RAB korkusudur bilgeliğin temeli. Akıl Kutsal Olan'ı tanımaktır.
11 Gama ta wurina kwanakinka za su yi yawa, za a kuwa ƙara wa ranka shekaru.
Benim sayemde günlerin çoğalacak, Ömrüne yıllar katılacak.
12 In kana da hikima, hikimarka za tă ba ka lada; in kai mai ba’a ne, kai kaɗai za ka sha wahala.”
Bilgeysen, bilgeliğinin yararı sanadır, Alaycı olursan acısını yalnız sen çekersin.”
13 Wawancin mace a bayyane yake; ba ta da ɗa’a kuma ba ta da sani.
Akılsız kadın yaygaracı Ve saftır, hiçbir şey bilmez.
14 Takan zauna a ƙofar gidanta, a wurin zama a wurin mafi tsayi na birni,
Evinin kapısında, Kentin en yüksek yerinde bir iskemleye oturur; Yoldan geçenleri, Kendi yollarından gidenleri çağırmak için,
15 tana kira ga masu wucewa, waɗanda suke tafiya kai tsaye a hanyarsu.
16 “Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo cikin nan!” Tana ce wa marasa hankali.
“Kim safsa buraya gelsin” der. Sağduyudan yoksun olanlara da,
17 “Ruwan da aka sata ya fi daɗi; abincin da aka ci a ɓoye ya fi daɗi!”
“Çalıntı su tatlı, Gizlice yenen yemek lezzetlidir” der.
18 Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol )
Ne var ki, evine girenler ölüme gittiklerini, Ona konuk olanlar Ölüler diyarının dibine indiklerini bilmezler. (Sheol )