< Karin Magana 9 >
1 Hikima ta gina gidanta; ta yi ginshiƙansa bakwai.
Wisdom hath built her house, she hath hewn out her seven pillars;
2 Ta shirya abincinta gauraye da ruwan inabinta; ta kuma shirya teburinta.
she hath slaughtered her cattle, she hath mingled her wine, she hath also prepared her table;
3 Ta aiki bayinta mata, tana kuma kira daga wurare masu tsayi na birnin.
she hath sent forth her maidens: she crieth upon the summits of the high places of the city,
4 “Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo nan ciki!” Tana faɗa wa marasa hankali.
Whoso is simple, let him turn in hither. To him that is void of understanding, she saith,
5 “Ku zo, ku ci abincina da ruwan inabin da na gauraye.
Come, eat ye of my bread, and drink of the wine that I have mingled.
6 Ku bar hanyoyinku marasa hankali za ku kuwa rayu; yi tafiya a hanyar fahimi.
Forsake follies and live, and go in the way of intelligence.
7 “Duk wanda ya yi wa mai ba’a gyara yana gayyatar zagi duk wanda ya tsawata wa mugu yakan gamu da cin mutunci.
He that instructeth a scorner getteth to himself shame; and he that reproveth a wicked [man] [getteth] to himself a blot.
8 Kada ka tsawata wa masu ba’a gama za su ƙi ka; ka tsawata wa mai hikima zai kuwa ƙaunace ka.
Reprove not a scorner, lest he hate thee; reprove a wise [man], and he will love thee.
9 Ka koya wa mai hikima zai kuwa ƙara hikima; ka koya wa mai adalci zai kuwa ƙara koyonsa.
Impart to a wise [man], and he will become yet wiser; teach a righteous [man], and he will increase learning.
10 “Tsoron Ubangiji shi ne mafarin hikima, sanin Mai Tsarki kuwa fahimi ne.
The fear of Jehovah is the beginning of wisdom; and the knowledge of the Holy is intelligence.
11 Gama ta wurina kwanakinka za su yi yawa, za a kuwa ƙara wa ranka shekaru.
For by me thy days shall be multiplied, and years of life shall be added to thee.
12 In kana da hikima, hikimarka za tă ba ka lada; in kai mai ba’a ne, kai kaɗai za ka sha wahala.”
If thou art wise, thou shalt be wise for thyself; and if thou scornest, thou alone shalt bear it.
13 Wawancin mace a bayyane yake; ba ta da ɗa’a kuma ba ta da sani.
The foolish woman is clamorous; she is stupid, and knoweth nothing.
14 Takan zauna a ƙofar gidanta, a wurin zama a wurin mafi tsayi na birni,
And she sitteth at the entry of her house, on a seat in the high places of the city,
15 tana kira ga masu wucewa, waɗanda suke tafiya kai tsaye a hanyarsu.
to call passers-by who go right on their ways:
16 “Bari dukan waɗanda suke marasa azanci su zo cikin nan!” Tana ce wa marasa hankali.
Whoso is simple, let him turn in hither. And to him that is void of understanding she saith,
17 “Ruwan da aka sata ya fi daɗi; abincin da aka ci a ɓoye ya fi daɗi!”
Stolen waters are sweet, and the bread of secrecy is pleasant.
18 Amma ba su san cewa matattu suna a can ba, cewa baƙinta suna a can cikin zurfin kabari ba. (Sheol )
But he knoweth not that the dead are there; [that] her guests are in the depths of Sheol. (Sheol )