< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
¿No clama la sabiduría; y la inteligencia da su voz?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
En los altos cabezos, junto al camino, a las encrucijadas de las veredas se para:
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
En el lugar de las puertas, a la entrada de la ciudad: a la entrada de las puertas da voces:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
O! hombres, a vosotros clamo; y mi voz es a los hijos de los hombres.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Entendéd simples astucia; y vosotros insensatos, tomád entendimiento:
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Oíd, porque hablaré cosas excelentes, y abriré mis labios para cosas rectas.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Porque mi paladar hablará verdad; y mis labios abominan la impiedad.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
En justicia son todas las razones de mi boca: no hay en ellas cosa perversa, ni torcida.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Todas ellas son rectas al que entiende; y rectas a los que han hallado sabiduría.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Recibíd mi castigo, y no la plata; y ciencia, mas que el oro escogido.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Porque mejor es la sabiduría que las piedras preciosas; y todas las cosas que se pueden desear, no se pueden comparar a ella.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Yo, la sabiduría, moré con la astucia; y yo invento la ciencia de los consejos.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
El temor de Jehová es aborrecer el mal; la soberbia, y la arrogancia, y el mal camino, y la boca perversa aborrezco.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Conmigo está el consejo, y el ser: yo soy la inteligencia; mía es la fortaleza.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Por mí reinan los reyes, y los príncipes determinan justicia.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Por mí dominan los príncipes, y todos los gobernadores juzgan la tierra.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Yo amo a los que me aman; y los que me buscan, me hallan.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Las riquezas y la honra están conmigo, riqueza firme y justa.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Mejor es mi fruto que el oro, y que el oro refinado; y mi renta, que la plata escogida.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Por vereda de justicia guiaré, por medio de veredas de juicio.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
Para hacer heredar a mis amigos el ser, y que yo hincha sus tesoros.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Jehová me poseyó en el principio de su camino, desde entonces, antes de sus obras.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Eternalmente tuve el principado, desde el principio, antes de la tierra.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Antes de los abismos fui engendrada; antes que fuesen las fuentes de las muchas aguas:
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Antes que los montes fuesen fundados: antes de los collados, yo era engendrada.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
No había aun hecho la tierra, ni las plazas, ni la cabeza de los polvos del mundo.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Cuando componía los cielos, allí estaba yo; cuando señalaba por compás la sobrehaz del abismo:
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
Cuando afirmaba los cielos arriba: cuando afirmaba las fuentes del abismo:
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
Cuando ponía a la mar su estatuto; y a las aguas, que no pasasen su mandamiento: cuando señalaba los fundamentos de la tierra:
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Con él estaba yo por ama, y fui en delicias todos los días, teniendo solaz delante de él en todo tiempo.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Tengo solaz en la redondez de su tierra; y mis solaces son con los hijos de los hombres.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Ahora pues, hijos, oídme; y bienaventurados los que guardaren mis caminos.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Obedecéd la instrucción, y sed sabios; y no la menospreciéis.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Bienaventurado el hombre que me oye, trasnochando a mis puertas cada día: guardando los umbrales de mis entradas.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Porque el que me hallare, hallará la vida; y alcanzará la voluntad de Jehová.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Mas el que peca contra mí, defrauda a su alma: todos los que me aborrecen, aman la muerte.

< Karin Magana 8 >