< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
¿No llama la sabiduría? ¿No alza su voz el entendimiento?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
En lo alto de la colina, se pone en pie junto al camino, y sobre en las encrucijadas.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
A las puertas de la ciudad, en la entrada grita:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
“¡Los estoy llamando a todos ustedes! ¡A todos los habitantes del mundo!
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Si eres inmaduro, aprende a crecer. Si eres tonto, aprende y vuélvete inteligente.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Escúchame porque tengo valiosas cosas que explicarte.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Yo digo lo correcto, porque digo la verdad y odio la maldad en todas sus formas.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Todas mis palabras son verdaderas, y ninguna es falsa ni engañosa.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Mis palabras son fáciles de entender para todo el que tiene entendimiento. Son rectas para el que tiene conocimiento.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Elige mi enseñanza por encima de la plata; elige el conocimiento más que el oro puro.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Porque la sabiduría es más valiosa que los rubíes. ¡Nada de lo que puedas desear se compara a ella!
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
“Yo, la sabiduría, vivo con las buenas decisiones. Sé como hallar el conocimiento y el discernimiento.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Honrar al Señor significa aborrecer el mal. Por ello aborrezco el orgullo y la arrogancia, la conducta malvada y el decir mentiras.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Tengo el consejo y el buen juicio. Conmigo está la inteligencia y el poder.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Gracias a mi los reyes reinan, y los gobernantes emiten decretos justos.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Gracias a mi los líderes y nobles pueden gobernar, así como todos los que gobiernan con justicia.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Amo a los que me aman, y los que me buscan de corazón me encontrarán.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Conmigo está la riqueza y el honor, así como la riqueza y prosperidad duraderas.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
El fruto que produzco es mejor que el oro, incluso que el oro puro, y mi cosecha es mejor que la plata más fina.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Vivo con rectitud, y sigo los caminos de la justicia.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
Yo otorgo riqueza a los que me aman, y lleno sus almacenes de tesoros.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
“El Señor me creó desde el principio. Fui creada antes que cualquier otra cosa.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Fui formada hace mucho tiempo, desde el principio, y antes de que el mundo existiera.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Nací cuando no había profundidades en el océano, cuando no había fuentes de aguas.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Nací antes de que se formaran las montañas y colinas,
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
aun antes de que él hiciera la tierra y sus campos, o siquiera el polvo de la tierra.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Estuve allí cuando los cielos fueron puestos en su lugar, cuando él dibujó el horizonte sobre el océano,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
cuando puso las nubes arriba en el cielo, y cuando creó las fuentes de los océanos.
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
Cuando estableció los límites del mar para que no se saliera más allá de su voluntad, y cuando estableció los fundamentos de la tierra.
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
En ese tiempo estaba a su lado, como maestro artesano. Lo alegraba todos los días, y yo sentía siempre alegría en su presencia.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Estuve muy feliz en el mundo que creó, y celebrábamos juntos con los seres humanos.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
“Ahora, hijos míos, escúchenme, porque los que siguen mis caminos son felices.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Escuchen mis instrucciones y sean sabios. No rechacen mi instrucción
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Felices son los que me escuchan, los que están pendientes en mi puerta para verme llegar.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Porque los que me encuentran, encuentran la vida, y son aceptados por el Señor.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Pero los que no me encuentran se hacen daño a sí mismos, pues todos los que me aborrecen aman la muerte”.