< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
آیا حکمت ندا نمی کند، و فطانت آوازخود را بلند نمی نماید؟۱
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
به‌سر مکان های بلند، به کناره راه، در میان طریقها می‌ایستد.۲
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
به‌جانب دروازه‌ها به دهنه شهر، نزد مدخل دروازه‌ها صدا می‌زند.۳
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
که شما را‌ای مردان می‌خوانم و آواز من به بنی آدم است.۴
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
‌ای جاهلان زیرکی را بفهمید و‌ای احمقان عقل رادرک نمایید.۵
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
بشنوید زیرا که به امور عالیه تکلم می‌نمایم و گشادن لبهایم استقامت است.۶
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
دهانم به راستی تنطق می‌کند و لبهایم شرارت را مکروه می‌دارد.۷
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
همه سخنان دهانم بر‌حق است و درآنها هیچ‌چیز کج یا معوج نیست.۸
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
تمامی آنهانزد مرد فهیم واضح است و نزد یابندگان معرفت مستقیم است.۹
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
تادیب مرا قبول کنید و نه نقره را، و معرفت را بیشتر از طلای خالص.۱۰
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
زیرا که حکمت از لعلها بهتر است، و جمیع نفایس را به او برابر نتوان کرد.۱۱
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
من حکمتم و در زیرکی سکونت دارم، و معرفت تدبیر را یافته‌ام.۱۲
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
ترس خداوند، مکروه داشتن بدی است. غرور و تکبر وراه بد و دهان دروغگو را مکروه می‌دارم.۱۳
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
مشورت و حکمت کامل از آن من است. من فهم هستم و قوت از آن من است.۱۴
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
به من پادشاهان سلطنت می‌کنند، و داوران به عدالت فتوا می‌دهند.۱۵
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
به من سروران حکمرانی می‌نمایند و شریفان و جمیع داوران جهان.۱۶
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
من دوست می‌دارم آنانی را که مرا دوست می‌دارند. وهر‌که مرا به جد و جهد بطلبد مرا خواهد یافت.۱۷
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
دولت و جلال با من است. توانگری جاودانی وعدالت.۱۸
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
ثمره من از طلا و زر ناب بهتر است، وحاصل من از نقره خالص.۱۹
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
در طریق عدالت می‌خرامم، در میان راههای انصاف،۲۰
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
تا مال حقیقی را نصیب محبان خود گردانم، وخزینه های ایشان را مملو سازم.۲۱
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
خداوند مرا مبداء طریق خود داشت، قبل از اعمال خویش از ازل.۲۲
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
من از ازل برقرار بودم، از ابتدا پیش از بودن جهان.۲۳
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
هنگامی که لجه هانبود من مولود شدم، وقتی که چشمه های پر ازآب وجود نداشت.۲۴
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
قبل از آنگاه کوهها برپاشود، پیش از تلها مولود گردیدم.۲۵
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
چون زمین وصحراها را هنوز نساخته بود، و نه اول غبار ربع مسکون را.۲۶
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
وقتی که او آسمان را مستحکم ساخت من آنجا بودم، و هنگامی که دایره را برسطح لجه قرار داد.۲۷
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
وقتی که افلاک را بالااستوار کرد، و چشمه های لجه را استوار گردانید.۲۸
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
چون به دریا حد قرار داد، تا آبها از فرمان اوتجاوز نکنند، و زمانی که بنیاد زمین را نهاد.۲۹
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
آنگاه نزد او معمار بودم، و روزبروز شادی می‌نمودم، و همیشه به حضور او اهتزاز می‌کردم.۳۰
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
و اهتزاز من در آبادی زمین وی، و شادی من بابنی آدم می‌بود.۳۱
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
پس الان‌ای پسران مرا بشنوید، وخوشابحال آنانی که طریقهای مرا نگاه دارند.۳۲
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
تادیب را بشنوید و حکیم باشید، و آن را ردمنمایید.۳۳
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
خوشابحال کسی‌که مرا بشنود، و هرروز نزد درهای من دیده بانی کند، و باهوهای دروازه های مرا محافظت نماید.۳۴
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
زیرا هر‌که مرایابد حیات را تحصیل کند، و رضامندی خداوندرا حاصل نماید.۳۵
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
و اما کسی‌که مرا خطا کند، به‌جان خود ضرر رساند، و هر‌که مرا دشمن دارد، موت را دوست دارد.۳۶

< Karin Magana 8 >