< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
[Numquid non sapientia clamitat, et prudentia dat vocem suam?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
In summis excelsisque verticibus supra viam, in mediis semitis stans,
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
juxta portas civitatis, in ipsis foribus loquitur, dicens:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
O viri, ad vos clamito, et vox mea ad filios hominum.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Intelligite, parvuli, astutiam, et insipientes, animadvertite.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Audite, quoniam de rebus magnis locutura sum, et aperientur labia mea ut recta prædicent.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Veritatem meditabitur guttur meum, et labia mea detestabuntur impium.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Justi sunt omnes sermones mei: non est in eis pravum quid, neque perversum;
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
recti sunt intelligentibus, et æqui invenientibus scientiam.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Accipite disciplinam meam, et non pecuniam; doctrinam magis quam aurum eligite:
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
melior est enim sapientia cunctis pretiosissimis, et omne desiderabile ei non potest comparari.]
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
[Ego sapientia, habito in consilio, et eruditis intersum cogitationibus.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Timor Domini odit malum: arrogantiam, et superbiam, et viam pravam, et os bilingue, detestor.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Meum est consilium et æquitas; mea est prudentia, mea est fortitudo.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Per me reges regnant, et legum conditores justa decernunt;
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
per me principes imperant, et potentes decernunt justitiam.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Ego diligentes me diligo, et qui mane vigilant ad me, invenient me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Mecum sunt divitiæ et gloria, opes superbæ et justitia.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Melior est enim fructus meus auro et lapide pretioso, et genimina me argento electo.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
In viis justitiæ ambulo, in medio semitarum judicii:
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
ut ditem diligentes me, et thesauros eorum repleam.]
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
[Dominus possedit me in initio viarum suarum antequam quidquam faceret a principio.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Ab æterno ordinata sum, et ex antiquis antequam terra fieret.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Nondum erant abyssi, et ego jam concepta eram: necdum fontes aquarum eruperant,
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
necdum montes gravi mole constiterant: ante colles ego parturiebar.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Adhuc terram non fecerat, et flumina, et cardines orbis terræ.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Quando præparabat cælos, aderam; quando certa lege et gyro vallabat abyssos;
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
quando æthera firmabat sursum, et librabat fontes aquarum;
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
quando circumdabat mari terminum suum, et legem ponebat aquis, ne transirent fines suos; quando appendebat fundamenta terræ:
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
cum eo eram, cuncta componens. Et delectabar per singulos dies, ludens coram eo omni tempore,
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
ludens in orbe terrarum; et deliciæ meæ esse cum filiis hominum.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Nunc ergo, filii, audite me: beati qui custodiunt vias meas.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Audite disciplinam, et estote sapientes, et nolite abjicere eam.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Beatus homo qui audit me, et qui vigilat ad fores meas quotidie, et observat ad postes ostii mei.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Qui me invenerit, inveniet vitam, et hauriet salutem a Domino.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Qui autem in me peccaverit, lædet animam suam; omnes qui me oderunt diligunt mortem.]

< Karin Magana 8 >