< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Dengar! Kebijaksanaan berseru-seru, hikmat mengangkat suara.
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Ia berdiri di bukit-bukit di sisi jalan, dan di persimpangan-persimpangan.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Di pintu gerbang, di jalan masuk ke kota, di situlah terdengar suaranya.
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
"Hai, umat manusia, kepadamu aku berseru; setiap insan di bumi, perhatikanlah himbauanku!
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Kamu yang belum berpengalaman, belajarlah mempunyai pikiran yang tajam; kamu yang bebal, belajarlah menjadi insaf.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Perhatikanlah perkataan-perkataanku, karena semuanya tepat dan bermutu.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Yang kukatakan, betul semua, sebab aku benci kepada dusta.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Perkataan-perkataanku jujur semua, tak satu pun yang berbelit atau salah.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Bagi orang cerdas, perkataanku benar, bagi orang yang arif, perkataanku tepat.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Hargailah nasihatku melebihi perak asli, pentingkanlah pengetahuan melebihi emas murni.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Akulah hikmat, lebih berharga dari berlian; tak dapat dibandingkan dengan apa pun yang kauidamkan.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Akulah hikmat; padaku ada pengertian, kebijaksanaan dan pengetahuan.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Menghormati TUHAN berarti membenci kejahatan; aku tidak menyukai kesombongan dan keangkuhan. Aku benci tingkah laku yang jahat dan kata-kata tipu muslihat.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Akulah yang memberi ilham. Dan aku juga yang mewujudkannya. Aku cerdas dan kuat pula.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Raja-raja kubantu menjalankan pemerintahan, para penguasa kutolong menegakkan keadilan.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Karena jasaku, para pembesar dan para bangsawan memerintah dan menjalankan keadilan.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Aku mengasihi mereka yang suka kepadaku; yang mencari aku, akan menemukan aku.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Padaku tersedia kekayaan juga kehormatan dan kemakmuran.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Yang kaudapat dari aku melebihi emas murni; lebih berharga dari perak asli.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Aku mengikuti jalan keadilan, aku melangkah di jalan kejujuran.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
Orang yang mengasihi aku, kujadikan kaya; kupenuhi rumahnya dengan harta benda.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Aku diciptakan TUHAN sebagai yang pertama, akulah hasil karya-Nya yang semula pada zaman dahulu kala.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Aku dibentuk sejak permulaan zaman, pada mulanya, sebelum bumi diciptakan.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Aku lahir sebelum tercipta samudra raya, sebelum muncul sumber-sumber air.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Aku lahir sebelum gunung-gunung ditegakkan, sebelum bukit-bukit didirikan,
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
sebelum TUHAN menciptakan bumi dan padang-padangnya, bahkan sebelum diciptakan-Nya gumpalan tanah yang pertama.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Aku menyaksikan ketika langit dihamparkan, dan cakrawala direntangkan di atas lautan,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
ketika TUHAN menempatkan awan di angkasa, dan membuka sumber-sumber samudra,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
ketika Ia memerintahkan air laut supaya jangan melewati batas-batasnya. Aku pun turut hadir di sana ketika alas bumi diletakkan-Nya.
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Aku berada di samping-Nya sebagai anak kesayangan-Nya, setiap hari akulah kebahagiaan-Nya; selalu aku bermain-main di hadapan-Nya.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Aku bersenang-senang di atas bumi-Nya, dan merasa bahagia di antara manusia.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Karena itu, dengarkanlah aku, hai orang muda! Turutilah petunjukku, maka kau akan bahagia.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Terimalah petuah dan jadilah bijaksana, janganlah engkau meremehkannya.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Bahagialah orang yang mendengarkan aku yang setiap hari duduk menanti di pintu rumahku, dan berjaga-jaga di gerbang kediamanku.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Siapa mendapat aku, memperoleh kehidupan, kepadanya TUHAN berkenan.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Siapa tidak mendapat aku, merugikan diri sendiri; orang yang membenciku, mencintai maut."