< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Ruft nicht die Weisheit laut, und läßt nicht die Klugheit ihre Stimme vernehmen?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Oben auf den Höhen, draußen auf dem Wege, mitten auf den Straßen hat sie sich aufgestellt;
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
zur Seite der Tore, am Ausgang der Stadt, beim Eingang der Pforten ruft sie laut:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
An euch, ihr Männer, ergeht mein Ruf, und meine Stimme an die Menschenkinder!
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Ihr Einfältigen, werdet klug, und ihr Toren, brauchet den Verstand!
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Höret, denn ich habe Vortreffliches zu sagen, und meine Lippen öffnen sich für das, was gerade ist.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Denn mein Gaumen redet Wahrheit, aber meine Lippen verabscheuen loses Geschwätz.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Alle Reden meines Mundes sind gerecht, es ist nichts Verkehrtes noch Verdrehtes darin.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Den Verständigen sind sie ganz recht, und wer Erkenntnis sucht, findet sie richtig.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Nehmet meine Zucht an und nicht Silber, und Erkenntnis lieber als feines Gold.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Ja, Weisheit ist besser als Perlen, und keine Kleinodien sind ihr zu vergleichen.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Ich, die Weisheit, wohne bei dem Scharfsinn und gewinne die Erkenntnis wohldurchdachter Pläne.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Die Furcht des HERRN ist ein Hassen des Bösen; Stolz und Übermut, schlechten Wandel und ein verdrehtes Maul hasse ich.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Von mir kommt Rat und Tüchtigkeit; ich bin verständig, mein ist die Kraft.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Durch mich herrschen die Könige und erlassen die Fürsten gerechte Verordnungen.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Durch mich regieren die Herrscher und die Edeln, alle Richter auf Erden.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Ich liebe, die mich lieben, und die mich frühe suchen, finden mich.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Reichtum und Ehre kommen mit mir, bedeutendes Vermögen und Gerechtigkeit.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Meine Frucht ist besser als Gold, ja als feines Gold, und was ich einbringe, übertrifft auserlesenes Silber.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Ich wandle auf dem Pfade der Gerechtigkeit, mitten auf der Bahn des Rechts,
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
auf daß ich meinen Liebhabern ein wirkliches Erbteil verschaffe und ihre Schatzkammern fülle.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Der HERR besaß mich am Anfang seiner Wege, ehe er etwas machte, vor aller Zeit.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Ich war eingesetzt von Ewigkeit her, vor dem Anfang, vor dem Ursprung der Erde.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Als noch keine Fluten waren, ward ich geboren, als die wasserreichen Quellen noch nicht flossen.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Ehe die Berge eingesenkt wurden, vor den Hügeln ward ich geboren.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Als er die Erde noch nicht gemacht hatte und was außerhalb [derselben liegt], die ganze Summe des Weltenstaubs,
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
als er den Himmel abzirkelte, war ich dabei; als er auf dem Meeresspiegel den Horizont abgrenzte,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
als er die Wolken droben befestigte und die Brunnen der Tiefe mauerte;
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
als er dem Meer seine Schranke setzte, damit die Wasser seinen Befehl nicht überschritten, als er den Grund der Erde legte,
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
da stand ich ihm als Werkmeister zur Seite und zu seinem Entzücken Tag für Tag und spielte vor seinem Angesicht allezeit;
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
ich spielte auf seinem Erdkreis und hatte mein Ergötzen an den Menschenkindern.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Und nun, ihr Söhne, gehorchet mir! Wohl denen, die meine Wege bewahren!
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Gehorchet der Zucht und werdet weise und seid nicht zügellos!
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Wohl dem Menschen, der mir also gehorcht, daß er täglich an meiner Pforte wacht und die Pfosten meiner Tür hütet;
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
denn wer mich findet, der findet das Leben und erlangt Gnade von dem HERRN;
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
wer mich aber verfehlt, schadet seiner eigenen Seele; alle, die mich hassen, lieben den Tod!

< Karin Magana 8 >