< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Horch! Die Weisheit ruft vernehmlich, und die Einsicht läßt ihre Stimme erschallen!
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Oben auf den Höhen am Wege, da wo die Pfade zusammenlaufen, hat sie sich aufgestellt;
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
neben den Toren, am Ausgang der Stadt, am Eingang der Pforten ruft sie laut:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
»An euch, ihr Männer, richte ich meinen Ruf, und meine Stimme ergeht an die Menschenkinder.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Gewinnt, ihr Einfältigen, Einsicht in Klugheit, und ihr Toren, gewinnt Einsicht in Verständigkeit!
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hört zu! Denn ich habe Wertvolles zu sagen, und meine Lippen will ich auftun zu (auf-) richtiger Rede;
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
denn mein Mund spricht Wahrheit aus, und Unehrlichkeit ist ein Greuel für meine Lippen.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Aufrichtig sind alle Reden meines Mundes: es ist nichts Hinterlistiges und Trügerisches in ihnen;
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
sie sind sämtlich klar für den Verständigen und richtig für die zur Erkenntnis Gelangten.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Nehmt Unterweisung lieber an als Silber, und Erkenntnis lieber als auserlesenes Gold!
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Denn die Weisheit ist besser als Korallen, und alle Kleinode kommen ihr nicht gleich.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Ich, die Weisheit, stehe im Bunde mit der Klugheit und verfüge über Erkenntnis wohldurchdachter Pläne.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Die Furcht des HERRN besteht im Haß gegen das Böse; Hoffart, Hochmut und bösen Wandel sowie den Mund des Truges hasse ich.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Mir steht kluger Rat und Überlegung zu Gebot, ich verfüge über Einsicht, und ich besitze Tatkraft.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Durch mich üben die Könige ihre Königsmacht aus und erlassen die Machthaber gerechte Verordnungen;
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
durch mich betätigen sich die Herrscher als Herrscher und alle Richter auf Erden als Edle.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Ich liebe, die mich lieben, und wer mich eifrig sucht, der findet mich.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Reichtum und Ehre sind bei mir zu finden, bleibender Wohlstand und Gerechtigkeit;
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
was ich einbringe, ist wertvoller als feines, gediegenes Gold, und mein Ertrag kostbarer als auserlesenes Silber.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Ich wandle auf dem Pfade der Gerechtigkeit, mitten auf den Bahnen des Rechts,
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
um denen, die mich lieben, bleibenden Besitz zu verschaffen und ihre Schatzkammern zu füllen.«
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
»Der HERR hat mich geschaffen als den Erstling seiner Schöpfertätigkeit, als das früheste seiner Werke in der Urzeit.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Von Ewigkeit her bin ich gebildet, von Anbeginn an, vor den Uranfängen der Erde.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Als noch keine Fluten der Tiefe da waren, bin ich geboren worden, ehe es wasserreiche Quellen gab.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Bevor die Berge eingesenkt waren, vor den Hügeln bin ich geboren worden,
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
als er die Erde und die Fluren noch nicht geschaffen hatte und die ersten Schollen des Erdreichs.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Als er den Himmel baute, war ich dabei, als er das Himmelsgewölbe feststellte über der weiten Urflut;
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
als er die Wolken droben befestigte, als er die Quellen aus den Fluten der Tiefe mit Macht hervorbrechen ließ;
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
als er dem Meer seine Grenze setzte, damit die Wasser seine Schranke nicht überschritten, als er die Grundpfeiler der Erde feststellte:
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
da war ich als Künstlerin ihm zur Seite und war voller Entzücken Tag für Tag, indem ich vor seinen Augen allezeit spielte,
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
indem ich auf seiner weiten Erdenwelt mein Spiel trieb und mein Entzücken an den Menschenkindern hatte.«
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
»Nun denn, ihr Söhne, höret auf mich! Denn glückselig sind, die meine Wege einhalten.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Höret auf meine Unterweisung, damit ihr weise werdet, und verwerft sie nicht!
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Wohl dem Menschen, der mir Gehör schenkt, indem er Tag für Tag an meiner Tür wacht und die Pfosten meiner Tore hütet!
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Denn wer mich findet, der findet das Leben und erlangt Wohlgefallen beim HERRN;
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
wer mich aber verfehlt, der fügt seiner eigenen Seele Schaden zu: alle, die mich hassen, lieben den Tod.«

< Karin Magana 8 >