< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Est-ce que la sagesse ne crie pas, et que la prudence ne fait pas entendre sa voix?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Sur les plus hauts et les plus élevés sommets, au-dessus de la voie, se tenant au milieu des sentiers,
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Près des portes de la cité, à l’entrée même de la ville, elle parle, disant:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
Ô hommes, c’est à vous que je crie, et ma voix s’adresse aux fils des hommes.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Apprenez, ô tout petits, la finesse, et vous, insensés, faites attention.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Ecoutez, car je vais parler de grandes choses, et mes lèvres s’ouvriront pour proclamer la droiture.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Ma bouche s’exercera à la vérité, et mes lèvres détesteront ce qui est impie.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Tous mes discours sont justes, il n’y a rien de dépravé ni de pervers.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
Ils sont droits pour ceux qui ont de l’intelligence, et équitables pour ceux qui trouvent la science.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Recevez ma discipline et non de l’argent: choisissez la doctrine plutôt que l’or.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Car mieux vaut la sagesse que toutes les choses les plus précieuses; et tout ce qu’il y a de désirable ne peut lui être comparé.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Moi, sagesse, j’habite dans le conseil, et je suis présente aux savantes pensées.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
La crainte du Seigneur hait le mal: l’arrogance et l’orgueil, une voie dépravée, et une langue double, je les déteste.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
À moi est le conseil et l’équité: à moi est la prudence, à moi est la force.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Par moi les rois règnent, et les législateurs décrètent des choses justes;
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Par moi les princes commandent, et les puissants rendent la justice.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Moi, j’aime ceux qui m’aiment, et ceux qui dès le matin veillent pour me chercher me trouveront.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Avec moi sont les richesses et la gloire, des biens superbes, et la justice.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Car mieux vaut mon fruit que l’or et les pierres précieuses, et mieux valent mes produits que l’argent le meilleur.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Je marche dans les voies de la justice, au milieu des sentiers du jugement,
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
Afin d’enrichir ceux qui m’aiment, et de remplir leurs trésors.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Le Seigneur m’a possédée au commencement de ses voies, avant qu’il fît quelque chose dès le principe.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Dès l’éternité j’ai été établie, dès les temps anciens, avant que la terre fût faite.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Les abîmes n’étaient pas encore, et moi déjà j’avais été conçue; les sources des eaux n’avaient pas encore jailli:
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Les montagnes à la pesante masse n’étaient pas encore affermies, et moi, avant les collines, j’étais engendrée:
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Il n’avait pas encore fait la terre et les fleuves, et les pôles du globe de la terre.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Quand il préparait les cieux, j’étais présente: quand par une loi inviolable il entourait d’un cercle les abîmes:
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
Quand il affermissait en haut la voûte éthérée, et qu’il mettait en équilibre les sources des eaux:
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
Quand il mettait autour de la mer ses limites, et qu’il imposait une loi aux eaux, afin qu’elles n’allassent point au-delà de leurs bornes; quand il pesait les fondements de la terre:
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
J’étais avec lui, disposant toutes choses; et je me réjouissais chaque jour, me jouant, en tout temps, devant lui:
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Me jouant dans le globe de la terre; et mes délices sont d’être avec les fils des hommes.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Maintenant donc, mes fils, écoutez-moi: Bienheureux ceux gardent mes voies.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Ecoutez la discipline, et soyez sages, et n’allez pas la rejeter.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Bienheureux l’homme qui m’écoute, et qui veille tous les jours à l’entrée de ma demeure, et se tient en observation auprès de ma porte.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Celui qui me trouvera trouvera la vie, et puisera le salut dan? le Seigneur:
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Mais celui qui péchera contre moi blessera son âme. Tous ceux qui me haïssent aiment la mort.