< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Does not Wisdom call out? Does not Understanding raise her voice?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
On the hilltops beside the road, at the crossroads, Wisdom has taken her stand.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Before the gates at the entrance into the city, at the entrances into the city, she calls out.
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
“It is to you, people, that I call; my voice is for the sons of mankind.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
You who are naive, learn wisdom; and you who are foolish, you must get an understanding mind.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Listen, because I will speak of noble things, and when my lips open I will say upright things.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For my mouth speaks what is trustworthy, and wickedness is disgusting to my lips.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
All the words of my mouth are just; in them is nothing twisted or misleading.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
All of them are straight for the person who understands; my words are upright for those who find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Acquire my instruction rather than silver; acquire knowledge rather than pure gold.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For Wisdom is better than jewels; no treasure is equal to her.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
I, Wisdom, live with Prudence, and I possess knowledge and discretion.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
The fear of Yahweh is to hate evil. I hate pride and arrogance, the evil way, and perverted speech. I hate them.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
I have good advice and sound wisdom; I am insight; strength belongs to me.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings reign, and rulers make laws that are just.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes rule, nobles, and all who govern with justice.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I love those who love me, and those who diligently seek me, find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
With me are riches and honor, lasting wealth and righteousness.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
My fruit is better than gold, even fine gold; my produce is better than pure silver.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
I walk in the path of righteousness, in the midst of the paths of justice.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
As a result, I make those who love me inherit wealth; I fill up their treasuries.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Yahweh created me at the beginning, the first of his deeds then.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
In ages long ago I was made—from the first, from the beginnings of the earth.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Before there were oceans, I was given birth— before there were springs abounding with water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before the mountains were settled and before the hills, I was born.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
I was born before Yahweh had made the earth or the fields, or even the first dust in the world.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
I was there when he established the heavens, when he drew a circle on the surface of the deep.
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
I was there when he established the clouds above and when the springs in the deep became fixed.
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
I was there when he made his limit for the sea, so the waters should not spread beyond his command, and when there was set the limit for the foundations of the dry land.
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
I was beside him, as a skilled craftsman; I was his delight day after day, always rejoicing before him.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
I was rejoicing in his whole world, and my delight was in the sons of mankind.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Now, my sons, listen to me, for those who keep my ways will be blessed.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Listen to my instruction and be wise; do not neglect it.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
The one who listens to me will be blessed. He will be watching every day at my doors, waiting beside the posts of my doors.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For whoever finds me, finds life, and he will find the favor of Yahweh.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
But he who fails, harms his own life; all who hate me love death.”

< Karin Magana 8 >