< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
¿ Not wisdom does she call out and understanding does she give forth? voice her.
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
At [the] top of [the] heights on [the] way between [the] pathways she stations herself.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
To [the] side of [the] gates to [the] opening of [the] town [the] entrance of [the] doorways they cry aloud.
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
To you O people I call and voice my [is] to [the] children of humankind.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
Understand O naive people prudence and O fools understand heart.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Listen for princely things I will speak and [the] utterance of lips my [will be] uprightness.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For truth it will utter palate my and [is] an abomination of lips my wickedness.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
[are] Righteousness all [the] words of mouth my there not among them [is] a twisted [thing] and a distorted [thing].
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
All of them [are] right to the discerning [person] and upright to [those who] find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Take discipline my and may not [you take] silver and knowledge more than gold chosen.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For [is] good wisdom more than jewels and all pleasures not they compare with it.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
I wisdom I dwell prudence and knowledge of discretion I find.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
[the] fear of Yahweh [is] to hate evil pride and arrogance - and a way evil and a mouth of perversities I hate.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
[belong] to Me counsel and sound wisdom I [am] understanding [belongs] to me strength.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings they reign and rulers they enact righteousness.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes they rule and noble [people] all judges of (righteousness. *L(H)*)
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I ([those who] love me *Q(K)*) I love and [those who] earnestly seek me they find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Wealth and honor [are] with me wealth enduring and righteousness.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
[is] good Fruit my more than gold and more than pure gold and gain my more than silver chosen.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
In [the] path of righteousness I walk in [the] midst of [the] pathways of justice.
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
To give as an inheritance [those who] love me - substance and treasuries their I fill.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Yahweh he created me [the] beginning of way his [the] beginning of works his from then.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
From long ago I was installed from [the] beginning from [the] beginnings of [the] earth.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
When there not [were] [the] deeps I was brought forth when there not [were] springs abounding of water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before mountains they were planted before [the] hills I was brought forth.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Until not he had made [the] earth and [the] open places and [the] first of [the] dusts of [the] world.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
When established he [the] heavens [was] there I when marked out he a circle on [the] surface of [the] deep.
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
When made firm he [the] clouds above when became strong [the] springs of [the] deep.
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
When set he for the sea - limit its and [the] waters not they will transgress mouth his when marked out he [the] foundations of [the] earth.
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
And I was beside him an artisan and I was delight day - day playing before him at every time.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Playing in [the] world of earth his and delight my [were] with [the] children of humankind.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
And therefore O children listen to me and how blessed! [are those who] ways my they observe.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Listen to correction and act wisely and may not you neglect [it].
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
How blessed! [is] a person [who] listens to me by keeping watch at doors my day - day by watching [the] doorposts of doorways my.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For [one who] finds me (he finds *Q(K)*) life and he obtained favor from Yahweh.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
And [one who] misses me [is] doing wrong to self his all [those who] hate me they love death.