< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Does not wisdom call out, and understanding raise her voice?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
On the heights overlooking the road, at the crossroads she takes her stand.
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Beside the gates to the city, at the entrances she cries out:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
“To you, O men, I call out, and my cry is to the sons of men.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
O simple ones, learn to be shrewd; O fools, gain understanding.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Listen, for I speak of noble things, and the opening of my lips will reveal right.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For my mouth will speak the truth, and wickedness is detestable to my lips.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
All the words of my mouth are righteous; none are crooked or perverse.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
They are all plain to the discerning, and upright to those who find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Receive my instruction instead of silver, and knowledge rather than pure gold.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For wisdom is more precious than rubies, and nothing you desire compares with her.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
I, wisdom, dwell together with prudence, and I find knowledge and discretion.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
To fear the LORD is to hate evil; I hate arrogant pride, evil conduct, and perverse speech.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Counsel and sound judgment are mine; I have insight and strength.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings reign, and rulers enact just laws;
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes rule, and all nobles who govern justly.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I love those who love me, and those who seek me early shall find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
With me are riches and honor, enduring wealth and righteousness.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
My fruit is better than gold, pure gold, and my harvest surpasses choice silver.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
I walk in the way of righteousness, along the paths of justice,
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
bestowing wealth on those who love me and making their treasuries full.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
The LORD created me as His first course, before His works of old.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
From everlasting I was established, from the beginning, before the earth began.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
When there were no watery depths, I was brought forth, when no springs were overflowing with water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before the mountains were settled, before the hills, I was brought forth,
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
before He made the land or fields, or any of the dust of the earth.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
I was there when He established the heavens, when He inscribed a circle on the face of the deep,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
when He established the clouds above, when the fountains of the deep gushed forth,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
when He set a boundary for the sea, so that the waters would not surpass His command, when He marked out the foundations of the earth.
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Then I was a skilled craftsman at His side, and His delight day by day, rejoicing always in His presence.
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
I was rejoicing in His whole world, delighting together in the sons of men.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Now therefore, my sons, listen to me, for blessed are those who keep my ways.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Listen to instruction and be wise; do not ignore it.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Blessed is the man who listens to me, watching daily at my doors, waiting at the posts of my doorway.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For whoever finds me finds life and obtains the favor of the LORD.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
But he who fails to find me harms himself; all who hate me love death.”