< Karin Magana 8 >

1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Doth not wisdom cry, And understanding put forth her voice?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
On the top of high places by the way, Where the paths meet, she standeth;
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
Beside the gates, at the entry of the city, At the coming in at the doors, she crieth aloud:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
Unto you, O men, I call; And my voice is to the sons of men.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
O ye simple, understand prudence; And, ye fools, be of an understanding heart.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hear, for I will speak excellent things; And the opening of my lips shall be right things.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
For my mouth shall utter truth; And wickedness is an abomination to my lips.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
All the words of my mouth are in righteousness; There is nothing crooked or perverse in them.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
They are all plain to him that understandeth, And right to them that find knowledge.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Receive my instruction, and not silver; And knowledge rather than choice gold.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
For wisdom is better than rubies; And all the things that may be desired are not to be compared unto it.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
I wisdom have made prudence my dwelling, And find out knowledge [and] discretion.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
The fear of Jehovah is to hate evil: Pride, and arrogancy, and the evil way, And the perverse mouth, do I hate.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Counsel is mine, and sound knowledge: I am understanding; I have might.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
By me kings reign, And princes decree justice.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
By me princes rule, And nobles, [even] all the judges of the earth.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
I love them that love me; And those that seek me diligently shall find me.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Riches and honor are with me; [Yea], durable wealth and righteousness.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
My fruit is better than gold, yea, than fine gold; And my revenue than choice silver.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
I walk in the way of righteousness, In the midst of the paths of justice;
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
That I may cause those that love me to inherit substance, And that I may fill their treasuries.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Jehovah possessed me in the beginning of his way, Before his works of old.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
I was set up from everlasting, from the beginning, Before the earth was.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
When there were no depths, I was brought forth, When there were no fountains abounding with water.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Before the mountains were settled, Before the hills was I brought forth;
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
While as yet he had not made the earth, nor the fields, Nor the beginning of the dust of the world.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
When he established the heavens, I was there: When he set a circle upon the face of the deep,
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
When he made firm the skies above, When the fountains of the deep became strong,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
When he gave to the sea its bound, That the waters should not transgress his commandment, When he marked out the foundations of the earth;
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Then I was by him, [as] a master workman; And I was daily [his] delight, Rejoicing always before him,
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
Rejoicing in his habitable earth; And my delight was with the sons of men.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Now therefore, [my] sons, hearken unto me; For blessed are they that keep my ways.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Hear instruction, and be wise, And refuse it not.
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Blessed is the man that heareth me, Watching daily at my gates, Waiting at the posts of my doors.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
For whoso findeth me findeth life, And shall obtain favor of Jehovah.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
But he that sinneth against me wrongeth his own soul: All they that hate me love death.

< Karin Magana 8 >