< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Mon ikke Visdommen kalder, løfter Indsigten ikke sin røst?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Oppe på Høje ved Vejen, ved Korsveje træder den frem;
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
ved Porte, ved Byens Udgang, ved Dørenes Indgang råber den:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
Jeg kalder på eder, I Mænd, løfter min Røst til Menneskens Børn.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
I tankeløse, vind jer dog Klogskab, I Tåber, så få dog Forstand!
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hør, thi jeg fører ædel Tale, åbner mine Læber med retvise Ord;
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
ja, Sandhed taler min Gane, gudløse Læber er mig en Gru.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
Rette er alle Ord af min Mund, intet er falskt eller vrangt;
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
de er alle ligetil for den kloge, retvise for dem der vandt Indsigt
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Tag ved Lære, tag ikke mod Sølv, tag mod Kundskab fremfor udsøgt Guld;
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
thi Visdom er bedre end Perler, ingen Skatte opvejer den
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Jeg, Visdom, er Klogskabs Nabo og råder over Kundskab og Kløgt.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
HERRENs Frygt er Had til det onde. Jeg hader Hovmod og Stolthed, den onde Vej og den falske Mund.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Jeg ejer Råd og Visdom, jeg har Forstand, jeg har Styrke.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Ved mig kan Konger styre og Styresmænd give retfærdige Love;
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
ved mig kan Fyrster råde og Stormænd dømme Jorden.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Jeg elsker dem, der elsker mig, og de, der søger mig, finder mig.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Hos mig er der Rigdom og Ære, ældgammelt Gods og Retfærd.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Min Frugt er bedre end Guld og Malme, min Afgrøde bedre end kosteligt Sølv.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Jeg vandrer på Retfærds Vej. midt hen ad Rettens Stier
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
for at tildele dem, der elsker mig, Gods og fylde deres Forrådshuse.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Mig skabte HERREN først blandt sine Værker, i Urtid, førend han skabte andet;
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
jeg blev frembragt i Evigheden, i Begyndelsen, i Jordens tidligste Tider;
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
jeg fødtes, før Verdensdybet var til, før Kilderne, Vandenes Væld, var til;
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
førend Bjergene sænkedes, før Højene fødtes jeg,
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
førend han skabte Jord og Marker, det første af Jordsmonnets Støv.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Da han grundfæsted Himlen, var jeg hos ham, da han satte Hvælv over Verdensdybet.
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
Da han fæstede Skyerne oventil og gav Verdensdybets Kilder deres faste Sted,
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
da han satte Havet en Grænse, at Vandene ej skulde bryde hans Lov, da han lagde Jordens Grundvold,
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
da var jeg Fosterbarn hos ham, hans Glæde Dag efter Dag; for hans Åsyn leged jeg altid,
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
leged på hans vide Jord og havde min Glæde af Menneskens Børn.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Og nu, I Sønner, hør mig! Vel den, der vogter på mine Veje!
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Hør på Tugt og bliv vise, lad ikke hånt derom!
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Lykkelig den, der hører på mig, så han daglig våger ved mine Døre og vogter på mine Dørstolper.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Thi den, der ftnder mig; finder Liv og opnår Yndest hos HERREN;
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
men den, som mister mig, skader sig selv; enhver, som hader mig, elsker Døden.