< Karin Magana 8 >
1 Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
Mon ikke Visdommen raaber, og Forstanden opløfter sin Røst?
2 A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
Paa Toppen af Højene ved Vejen, midt paa Stierne staar den;
3 kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
ved Siden af Portene, ved Udgangen af Staden, ved Indgangen til Portene raaber den:
4 “Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
Til eder, I Mænd, vil jeg raabe, og min Røst lyde til Menneskens Børn.
5 Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
I uvidende! fatter Vid; og I Daarer! fatter Forstand.
6 Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
Hører, thi jeg vil tale fyrstelige Ting og aabne mine Læber med Retvished.
7 Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
Thi min Gane taler Sandhed, og Ugudelighed er en Vederstyggelighed for mine Læber.
8 Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
I Retfærdighed ere alle min Munds Ord; der er intet fordrejet eller forvendt i dem.
9 Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
De ere alle rette for den forstandige og ligefremme for dem, som finde Kundskab.
10 Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
Tager imod min Undervisning og ikke imod Sølv og imod Kundskab fremfor udsøgt Guld.
11 gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
Thi Visdom er bedre end Perler, og alle de Ting, man har Lyst til, kunne ikke lignes ved den.
12 “Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
Jeg, Visdommen, jeg har taget Bolig i Vidskab og besidder Kundskab om kløgtige Raad.
13 Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
Herrens Frygt er at hade ondt; Hoffærdighed og Hovmodighed og Ondskabs Vej og den Mund, som taler forvendte Ting, hader jeg.
14 Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
Raad og hvad der har Bestand, hører mig til; jeg er Forstand, mig hører Styrke til.
15 Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
Ved mig regere Konger, og ved mig beskikke Fyrster Ret.
16 ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
Ved mig herske Herskere og Høvdinger, alle Dommere paa Jorden.
17 Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
Jeg elsker dem, som elske mig, og de, som søge mig, skulle finde mig.
18 Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
Rigdom og Ære er hos mig, varigt Gods og Retfærdighed.
19 ’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
Min Frugt er bedre end Guld og ædelt Malm, og at vinde mig er bedre end udsøgt Sølv.
20 Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
Jeg vandrer paa Retfærdigheds Vej, midt paa Rettens Stier,
21 ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
til at lade dem, som elske mig, arve varigt godt og til at fylde deres Forraadskamre.
22 “Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
Herren ejede mig som sin Vejs Begyndelse, forud for sine Gerninger, fra fordums Tid.
23 an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
Fra Evighed er jeg indsat, fra det første af, før Jorden var.
24 Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
Da Afgrundene endnu ikke vare, er jeg født, da Kilderne, som have meget Vand, ikke vare til.
25 kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
Før Bjergene bleve nedsænkede, før Højene bleve til, er jeg født.
26 kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
Han havde endnu ikke skabt Jorden eller Markerne eller det første af Jordens Støv.
27 Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
Der han beredte Himlene, da var jeg der, der han slog en Kreds oven over Afgrunden;
28 sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
der han befæstede Skyerne heroventil, der Afgrundens Kilder fik deres faste Sted;
29 sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
der han satte Havet dets Grænse, at Vandene ikke skulde overtræde hans Befaling, der han lagde Jordens Grundvold:
30 A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
Da var jeg hos ham som Kunstnerinde, og jeg var hans Lyst Dag for Dag, og jeg legede for hans Ansigt alle Tider;
31 ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
jeg legede i Verden paa hans Jord, og min Lyst var hos Menneskens Børn.
32 “Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
Og nu, Børn, hører mig! og salige ere de, som tage Vare paa mine Veje.
33 Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
Hører Undervisning og bliver vise, og lader den ikke fare!
34 Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
Saligt er det Menneske, som hører mig, saa at han dagligt vaager ved mine Døre og tager Vare paa mine Dørstolper.
35 Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
Thi hvo mig finder, han finder Livet og faar Velbehag hos Herren.
36 Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”
Men hvo, som synder imod mig, skader sin Sjæl; alle, som mig hade, elske Døden.