< Karin Magana 7 >
1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
Mein Sohn, bewahre meine Rede und birg meine Gebote in dir!
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Beobachte meine Gebote, so wirst du leben, und bewahre meine Lehre wie einen Augapfel!
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Binde sie an deine Finger, schreibe sie auf die Tafel deines Herzens!
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Sprich zur Weisheit: Du bist meine Schwester! und sage zum Verstand: Du bist mein Vertrauter!
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
daß du bewahrt bleibest vor dem fremden Weibe, vor der Buhlerin, die glatte Worte gibt!
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
Denn als ich am Fenster meines Hauses durch das Gitter guckte
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
und die Einfältigen beobachtete, bemerkte ich unter den Söhnen einen unverständigen Jüngling.
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
Der strich auf der Gasse herum, nicht weit von ihrem Winkel, und betrat den Weg zu ihrem Haus
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
in der Dämmerung, beim Einbruch der Nacht, da es dunkelte.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
Siehe, da lief ihm ein Weib entgegen im Hurenschmuck und verschmitzten Herzens,
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
frech und zügellos. Ihre Füße können nicht zu Hause bleiben;
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
bald auf der Straße, bald auf den Plätzen, an allen Ecken lauert sie.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
Die ergriff und küßte ihn, und mit unverschämter Miene sprach sie zu ihm:
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
«Ich war ein Dankopfer schuldig, heute habe ich meine Gelübde bezahlt;
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
darum bin ich ausgegangen dir entgegen, um eifrig dein Angesicht zu suchen, und ich fand dich auch!
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
Ich habe mein Lager mit Teppichen gepolstert, mit bunten Decken von ägyptischem Garn;
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
ich habe mein Bett besprengt mit Myrrhe, Aloe und Zimt.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
Komm, wir wollen der Liebe genießen bis zum Morgen, uns an Liebkosungen ergötzen!
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
Denn der Mann ist nicht zu Hause, er hat eine weite Reise angetreten,
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
er hat den Geldbeutel mitgenommen und kommt erst am Tage des Vollmonds wieder heim.»
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
Durch ihr eifriges Zureden machte sie ihn geneigt und bewog ihn mit ihren glatten Worten,
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
so daß er ihr plötzlich nachlief, wie ein Ochse zur Schlachtbank geht und wie ein Gefesselter zum Narrenhaus
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
(bis ihm der Pfeil die Leber spaltet), wie ein Vogel ins Netz hinein fliegt und nicht weiß, daß es ihn sein Leben kostet!
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
So schenkt mir nun Gehör, ihr Söhne, und merkt auf die Reden meines Mundes!
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Dein Herz neige sich nicht ihren Wegen zu, und verirre dich nicht auf ihre Pfade;
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
denn sie hat viele verwundet und zu Fall gebracht, und gewaltig ist die Zahl ihrer Opfer.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol )
Wege zur Unterwelt sind ihr Haus, führen hinab zu den Kammern des Todes! (Sheol )