< Karin Magana 7 >

1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
Mon fils, garde mes paroles; et mes préceptes, mets-les en réserve pour toi. Mon fils,
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Observe mes commandements et tu vivras; et garde ma loi comme la pupille de ton œil:
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Lie-la à tes doigts, écris-la sur les tables de ton cœur.
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Dis à la sagesse: Ma sœur; et la prudence, appelle-la ton amie:
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
Afin qu’elle te préserve d’une femme du dehors, et d’une étrangère, qui rend ses paroles douces.
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
Car de la fenêtre de ma maison par les barreaux, j’ai regardé,
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
Et je vois les petits enfants, je considère un jeune homme sans cœur,
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
Qui passe dans une rue au coin, et s’avance vers la maison de cette femme,
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
À la brume, sur le soir, dans les ténèbres de la nuit et une obscurité profonde.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
Et voilà qu’au-devant de lui va une femme d’une parure de courtisane, prête à ravir des âmes; causeuse et vagabonde,
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
Inquiète, ne pouvant dans sa maison se tenir sur ses pieds,
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
Tantôt dehors, tantôt dans les places publiques, tantôt aux coins des rues, tendant ses pièges.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
Et prenant le jeune homme, elle lui donne un baiser, et, d’un visage effronté, elle le flatte, disant:
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
J’avais voué des victimes pour ton salut; aujourd’hui j’ai acquitté mes vœux;
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
C’est pour cela que je suis sortie au-devant de toi, désirant te voir, et je t’ai rencontré.
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
J’ai entrelacé mon lit de sangles, j’y ai étendu des couvertures brodées d’Egypte;
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
J’ai parfumé ma couche de myrrhe, d’aloës et de cinnamome.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
Viens, enivrons-nous de délices, jouissons de ce que nous avons désiré, jusqu’à ce que le jour paraisse;
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
Mon mari n’est pas à sa maison: il est parti pour un voyage très long;
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
Il a pris avec lui le sac où est l’argent; c’est à la pleine lune qu’il doit revenir à sa maison.
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
Elle l’a enlacé par la multitude de ses paroles; et par les flatteries de ses lèvres, elle l’a entraîné.
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
Aussitôt, il la suit comme un bœuf conduit pour servir de victime, et comme un agneau bondissant et ignorant, l’insensé, qu’on l’entraîne pour le lier,
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
Jusqu’à ce qu’une flèche ait percé son foie; comme un oiseau va précipitamment dans un filet, ignorant qu’il s’agit du danger de son âme.
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
Maintenant donc, mon fils, écoute-moi, et sois attentif aux paroles de ma bouche.
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Que ton esprit ne soit point entraîné dans les voies de cette femme; ne t’égare pas dans ses sentiers;
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
Car elle a renversé beaucoup de blessés qu’elle avait faits, et les plus forts, quels qu’ils fussent, ont été tués par elle.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)
Ce sont des voies de l’enfer que sa maison; voies pénétrant jusque dans les profondeurs de la mort. (Sheol h7585)

< Karin Magana 7 >