< Karin Magana 7 >

1 Ɗana, ka kiyaye kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka.
Mon fils, retiens mes paroles, Et garde avec toi mes préceptes.
2 Ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu; ka tsare koyarwata kamar ƙwayar idonka.
Observe mes préceptes, et tu vivras; Garde mes enseignements comme la prunelle de tes yeux.
3 Ka daure su a yatsotsinka; ka rubuta su a allon zuciyarka.
Lie-les sur tes doigts, Écris-les sur la table de ton cœur.
4 Ka faɗa wa hikima, “Ke’yar’uwata ce,” ka kuma kira fahimi danginka;
Dis à la sagesse: Tu es ma sœur! Et appelle l’intelligence ton amie,
5 za su kiyaye ka daga mazinaciya, daga mace marar aminci da kalmominta masu ɗaukan hankali.
Pour qu’elles te préservent de la femme étrangère, De l’étrangère qui emploie des paroles doucereuses.
6 A tagar gidana na leƙa ta labule mai rammuka.
J’étais à la fenêtre de ma maison, Et je regardais à travers mon treillis.
7 Sai na gani a cikin marasa azanci, na lura a cikin samari, wani matashi wanda ba shi da hankali.
J’aperçus parmi les stupides, Je remarquai parmi les jeunes gens un garçon dépourvu de sens.
8 Yana gangarawa a titi kusa da kusurwarta, yana tafiya a gefen wajen gidanta
Il passait dans la rue, près de l’angle où se tenait une de ces étrangères, Et il se dirigeait lentement du côté de sa demeure:
9 da magariba, yayinda rana tana fāɗuwa, yayinda duhun dare yana farawa.
C’était au crépuscule, pendant la soirée, Au milieu de la nuit et de l’obscurité.
10 Sai ga mace ta fito don ta sadu da shi, saye da riga kamar karuwa shirye kuma don ta yaudare shi.
Et voici, il fut abordé par une femme Ayant la mise d’une prostituée et la ruse dans le cœur.
11 (Ba ta jin tsoro, ko kuma kunya, ƙafafunta ba sa zama a gida;
Elle était bruyante et rétive; Ses pieds ne restaient point dans sa maison;
12 wani lokaci a titi, wani lokaci a dandali, tana yawo a kowace kusurwa.)
Tantôt dans la rue, tantôt sur les places, Et près de tous les angles, elle était aux aguets.
13 Sai ta kama shi ta rungume shi da duban soyayya a fuskarta ta ce,
Elle le saisit et l’embrassa, Et d’un air effronté lui dit:
14 “Ina da hadaya ta salama a gida; yau zan cika alkawarina.
Je devais un sacrifice d’actions de grâces, Aujourd’hui j’ai accompli mes vœux.
15 Saboda haka na fito don in sadu da kai; na neme ka na kuma same ka!
C’est pourquoi je suis sortie au-devant de toi Pour te chercher, et je t’ai trouvé.
16 Na lulluɓe gadona da lili masu launi dabam-dabam daga Masar.
J’ai orné mon lit de couvertures, De tapis de fil d’Égypte;
17 Na yayyafa turare a gadona da mur, aloyes da kuma kirfa.
J’ai parfumé ma couche De myrrhe, d’aloès et de cinnamome.
18 Zo, mu sha zurfin ƙauna har safe; bari mu ji wa ranmu daɗi da ƙauna!
Viens, enivrons-nous d’amour jusqu’au matin, Livrons-nous joyeusement à la volupté.
19 Mijina ba ya gida; ya yi tafiya mai nisa.
Car mon mari n’est pas à la maison, Il est parti pour un voyage lointain;
20 Ya ɗauki jakarsa cike da kuɗi ba zai kuwa dawo gida ba sai tsakiyar wata.”
Il a pris avec lui le sac de l’argent, Il ne reviendra à la maison qu’à la nouvelle lune.
21 Da kalmomin rarrashi ta sa ya kauce; ta ɗauki hankalinsa da sulɓin maganarta.
Elle le séduisit à force de paroles, Elle l’entraîna par ses lèvres doucereuses.
22 Nan take, ya bi ta kamar saniyar da za a kai mayanka, kamar wawa zuwa wurin da za a ba shi horo
Il se mit tout à coup à la suivre, Comme le bœuf qui va à la boucherie, Comme un fou qu’on lie pour le châtier,
23 sai da kibiya ta soki hantarsa, kamar tsuntsun da ya ruga cikin tarko, ba tare da sani zai zama sanadin ransa ba.
Jusqu’à ce qu’une flèche lui perce le foie, Comme l’oiseau qui se précipite dans le filet, Sans savoir que c’est au prix de sa vie.
24 Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; ku kasa kunne ga abin da nake faɗa.
Et maintenant, mes fils, écoutez-moi, Et soyez attentifs aux paroles de ma bouche.
25 Kada ku bar zuciyarku ta juya zuwa hanyoyinta ko ku kauce zuwa hanyoyinta.
Que ton cœur ne se détourne pas vers les voies d’une telle femme, Ne t’égare pas dans ses sentiers.
26 Ta zama sanadin fāɗuwar yawanci; kisan da ta yi ba ta ƙidayuwa.
Car elle a fait tomber beaucoup de victimes, Et ils sont nombreux, tous ceux qu’elle a tués.
27 Gidanta babbar hanya ce zuwa kabari mai yin jagora zuwa ɗakunan lahira. (Sheol h7585)
Sa maison, c’est le chemin du séjour des morts; Il descend vers les demeures de la mort. (Sheol h7585)

< Karin Magana 7 >